• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Masu Sarrafa Waken Soya Na Neman A Haramta Fitar Da Shi Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sarrafa mai daga waken soya zuwa man girke-girke ta kasa (OSPAN), ta bayyana jarinta na dala miliyan 250 da ta zuba; don sarrafa mai daga Irin Waken Soya, a matsayin wanda ke fuskantar barazana, sakamakon yadda ake fitar da Waken Soyar zuwa kasashen waje.

Wannan korafin na kunshe ne a cikin sanarwar da Shugaban Kungiyar na Kasa, Sama’ila Barau Maigoro da Mataimakinsa, Mista  Hule Idyerkas suka sanya wa hannu tare da fitar da shi a Garin Lafiya da ke a Jihar Nasarawa.

  • Hizba Ta Gana Da Kungiyar Masu Bege, Ta Bukaci Su Tsabtace Harshe
  • Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Sanarwar ta yi kira da a haramta fitar da Waken Soya daga Nijeriya zuwa sauran kasashen ketare, domin a karfafa wadanda suke sarrafa Irin Waken Soyar zuwa man girki; kwarin guiwa.

A cewar sanarwar, idan aka sarrafa man daga Irin na Waken Soya zuwa man girki, hakan zai bayar da dama wajen sarrafa  ainahin danyen man Waken Soyar da za a rika yin amfani da shi a cikin kasar nan, wanda hakan zai taimaka wajen karya farashin sauran man girki a Nijeriya.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, akwai ‘ya’yan kungiyar manya da matsakaita da suka zuba jarinsu, domin sarrafa mai daga Irin Waken Soya zuwa man girki.

Labarai Masu Nasaba

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Ta kara da cewa, a yanzu haka man girkin da ake sarrafawa daga Irin Waken Soya a kowace shekara; ya kai tan miliyan uku, inda kuma jarin da aka zuba a fannin ya kai na kimanin dala miliyan 250.

A cewar sanarwar, a yanzu haka mune a kan gaba wajen samar da aikin yi a bangaren aikin noma na fadin kasar nan, domin muna samar da ayyuka na kai tsaye sama da 200,000.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, muna so Shugaban Kasa Bola Ahmed  Tinubu da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Doris Uzoka-Anite su sani cewa, akasarin masana’antun da ke sarrafa mai daga Irin Waken Soya zuwa man girke-girke a kasar nan, na ci gaba da kullewa sakamakon karancin kayan aiki, musamman Waken Soya.

Bugu da kari sanarwar ta bayyana cewa, Manoman Waken Soya a shekarar 2022; sun noma Waken Soya kimanin tan 680,000, amma maimakon su sayar da shi ga masu sarrafa shi a nan cikin gida, sai suka gwammace fitar da shi zuwa kasashen ketare; domin samun kazamar riba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, wannan lamarin na ci gaba da zama babbar barazana ga tattalin arzikin wannan kasa tare da jawo koma baya ga kokarin da gwamnatin kasar ke yi na fadada tattalin arziki da kuma kokarin samo wadanda za su zuba hannin jari a fannin tattalin arzikin tare da samar da ayyukan yi a fannin sarrafa Irin Waken Soya zuwa man girki.

Kungiyar ta sanar da cewa, Nijeriya ba ta cikin jerin kasashen duniyar da ke a kan gaba, wajen noman Waken Soya, inda wannan sabon halin na fitar da Waken Soya zuwa ketare ke jawo wa masu sarrafa mai daga Irin Waken Soya a kasar nan babban koma baya.

Kazalika, kungiyar ta OPSAN ta bukaci Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ta kawo musu daukin gaggawa a kan matsalar fitar da wannan Wake na Soya da ake yi zuwa kasashen waje.

Sannan, kungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta haramta fitar da Waken Soyar na wucin gadi daga nan Nijeriya zuwa sauran kasashen waje, har sai an tabbatar an samar da wadatuwarsa a fadin wannan kasa baki-daya.

Har ila yau, kungiyar ta kara da cewa, idan aka haramta fitar da Waken Soyar daga wannan kasa zuwa kasashen ketaren na wucin gadi, hakan zai taimaka wajen kara fadadawa da kuma bunkasa masana’antun da ke sarrafa Irin Waken Soyar zuwa na man girki a kasar nan tare da kara bunkasa tattalin arziki da kara samar da ayyukan yi  ga ‘yan kasa baki-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kammala Wasan  Karshen Damben Warriors  Na Wannan Shekarar A Kano

Next Post

Kula Da Tsaftar Hakori

Related

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

1 day ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

1 week ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

1 week ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

1 week ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Next Post
Kula Da Tsaftar Hakori

Kula Da Tsaftar Hakori

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta MiÆ™a SaÆ™on Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan ÆŠantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.