• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya

Ce-ce-ku-cen Da Aka Yi Kan Yawan Wakilan Nijeriya 

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Rawar Da Nijeriya Ta Taka A Taron Dumamar Yanayi Na Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya ta taka muhimmiyar rawa a taron dumamar yanayi na duniya (COP28), wanda ya gudana a Kasar Dubai.

Sai dai, ana ta faman caccakar gwamnatin tarayya dangane da yawan tawagar da suka wakilci Nijeriya a wannan babban taron.

  • An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Asibiti, Makaranta Da Gidaje Ga Al’ummar Tudun Biri – Gwamnan Kaduna

An rawaito cewa, Kasar Nijeriya ta tura wakilai har mutum 1,411, wadda ta kasance kasa ta uku a yawan kasashen da suka tura, domin halartar wannan taro.

Lamarin ya gamu da suka kwarai da gaske, musamman ganin yadda al’ummar Nijeriya ke ta fama da halin kaka-na-ka-yi, sakamakon halin matsatsin rayuwa da aka samu kai a ciki, tun bayan janye tallafin mai, inda masu ruwa da tsaki kuma suka soki matakin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu; kan wannan lamari.

A gefe guda kuma, Fadar Shugaban Kasa ta yi karin haske a kan wakilai 1,411, inda ta ce wadanda gwamnatin tarayya ta dauki nauyi, ba su kai mutum 100 a cikinsu ba.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Da yake tofa nasa albarkacin bakin, Dan Takarar Shugaban Kasa na Jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar, ya zargi Shugaba Tinubu da yin amfani da wannan taro na sauyin yanayi zuwa taron jam’iyya, a daidai irin wannan lokaci da al’ummar Nijeriya ke neman tabbatar da gaskiya da rikon amana.

Abubukar, a wata sanarwa da ke dauke da sa hannun Kakakinsa, Paul Ibe, ya kuma zargi Tinubu da barnatar da dukiyar kasa; duk kuwa da halin matsin da kasar ke ciki. Ya kara da cewa, duk gwamnatin da ta san abin da take yi, musamman a irin wannan lokacin, ba za ta taba fara yin yunkurin tura wakilai har sama da dubu wani taro ba.

Haka nan shi ma dan takarar Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi, ya bayyana yawan wakilai a matsayin asarar dukiyar al’ummar kasa.

A shafin Obin na Tiwita, ya ce, mafi yawan wadanda aka tura a matsayin wakilan, ba su da wata alaka da aikin gwamnati.

“Mafi yawan wadanda aka tura, babu abin da suka sani dangane da sauyin yanayi,” kamar yadda ya zarga.

Sannan, ya yi tir da matakin da cewa; a irin lokacin da al’ummar Nijeriya ke kan gwagwarmayar neman abincin da za su kai baki tare da matsin rayuwa da ya yi musu katutu, sai ga shi wannan gwamnati ta kwashi makuden kudade ta tura tulin wakilai zuwa wani taro a kasar waje.

Da yake mai da nasa martanin, babban mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren yada labarai, Temitope Ajayi, a wata sanarwar da ya fitar, ya bayyana cewa; ba dukkanin wakilan Nijeriya 1,411 a taron COP28 ne gwamnati ta dauki nauyinsu ba.

Ya ce, wakilan Nijeriya sun hada da bangarorin fararen hula, shugabannin ‘yan kasuwa, kwararru a bangaren muhalli, masana kan yanayi, ‘yan jarida da kuma jami’an gwamnati daga ma’aikatu da sassa daban-daban.

Duk da dai, bai bayyana adadin jami’an da gwamnatin ta dauki nauyin biyan kudin tafiyar tasu taron ba, sabanin jita-jitan da ake cewa; sun kai sama da wakilai 600 da gwamnati ta dauki nauyinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: COP28DubaiTawagar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matatar Dangote Ta Karbi Danyen Man Farko Da Za Ta Fara Tacewa

Next Post

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

9 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

11 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

12 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

13 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

16 hours ago
Next Post
Game Da Tambayar Nan:  Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

Game Da Tambayar Nan: Ko Ka Yi Tir Da Harin Ranar 7 Ga Oktoba?

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.