• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasar Nijeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta raba Naira miliyan 25 ga mabukata 250 ta hanyar shirin Renewed Hope Initiative Elderly Support Scheme (RHIESS) a Jihar Kebbi.

Sanata Oluremi Tinubu ta samu wakilcin uwargidan gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Idris, wadda ita ce ko’odinetan shirin na jihar a babban bugu na RHIESS a Birnin Kebbi.

  • Tinubu Ya Sake Bullo Da Shirin Ciyar Da Dalibai A Makarantu
  • Kotun Ƙoli Ta Kammala Sauraron Ƙarar Zaɓen Kano, Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci

Ta ce, “Wannan shirin ne na tallafa wa marasa galihu 250 ‘yan kasa da suke da shekaru 65 zuwa sama a fadin dukkan jahohin tarayya 36 hadi da babban birnin tarayya da kuma tsofaffi daga kungiyar matan jami’an tsaro na ‘yansanda (DEPOWA).

“Wadannan zababbun wadanda za su ci gajiyar shirin za su karbi kudi Naira 100,000 kowannensu, domin a rage musu radadin talaucin tabarbarewar tattalin arziki da kuma rage wa manyanmu da suke fama da bukata a rayuwasu.”

Matar Shugaban kasa, ta kara da cewa jimillar kudaden da aka fitar sun kai Naira miliyan 950 kamar yadda hukumar gudanarwar kungiyar Renewed Hope Initiative ta amince.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

A cewarta, kowace jiha ta tarayya za ta karbi kudi har Naira miliyan 25 don tallafa wa mutanen jiharsu.

“Mun himmatu wajen ganin kowace jiha ta samu wannan tallafi, ba tare da nuna wariyaba,” in ji ta.

Misis Oluremi Tinubu, wadda ta jaddada muhimmancin ba da fifiko ga tsofaffi a cikin shirin, ta ce kula da su wani bangare ne na girmama su da gudunmawar da suka bayar tare da amincewa da haduwar da suka fuskanta.

Haka zalika ta ce “Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta ba da kulawa ga manyan ‘yan kasarmu, haka kuma za a ba da fifiko ga kiwon lafiyarku, ilimin yara kananan, don rage muku walhalhalu rayuwa.

A wani bangare na tallafin da jihar ke bai wa shirin, sakatariyar dindindin ta ma’aikatar harkokin mata da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Aisha Maikurata, ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da tallafin ba da kiwon lafiya a kyauta tare da raba kayan abinci iri-iri ga dattawan jihar.

“Ma’aikatarmu tana tallafa wa tsofaffi, gajiyayyu da masara galihu da kuma masu karamin karfi a kyauta tare da rarraba sauran kayayyaki ga wadanda suka amfana kamar yadda ya kamata, don tabbatar da nasarar wannan shirin,” in ji ta.

Hajiya Aisha Maikurata ta gode wa uwargidan shugaban kasa da gwamnatin jihar da kuma uwargidan gwamnan bisa kokarinsu na ganin an samu nasarar raba wa wadanda suka ci gajiyar tallafin.

Da yake mika godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar, Alhaji Ahmad Mahmud, wanda ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, ya bayar da tabbacin cewa za a yi amfani da wannan karimcin cikin adalci domin cimma burin da aka sa a gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Nuna Fim Mai Taken “Peking Man, The Last Secret of Humankind” Karo Na Farko A Hedkwatar UNESCO

Next Post

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Related

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

43 minutes ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

3 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

4 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

5 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

6 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.