ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Majalisa

Majalisar Wakilai a ranar Talata, ta yanke shawarar yin bincike kan yadda aka yi watsi da cibiyoyin ci gaban masana’antu (IDC) sama da 30 a fadin kasar nan.

Majalisar ta umurci kwamitinta kan masana’antu da ya binciki yadda aka yi watsi da su tare da ba da shawarar yin amfani da cibiyoyin da suka dace don manufofinsu tare da bayar da rahoto cikin makonni hudu don ci gaba da aiwatar da doka.

  • NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
  • Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

Kudurin ya biyo bayan amincewa da kudirin da dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Onitsha ta Arewa/Kudu na Jihar Anambra, Hon. Emeka Idu, ya gabatar a zauren majalisa.

ADVERTISEMENT

Idu ya lura cewa an kafa IDC sama da 30 a shekarun 1970 tare da manufar ba da taimako ga kanana da matsakaitan masana’antu.

Dan majalisar ya ce duk da cibiyoyin shiyya hudu da ke Osogbo, Owerri, Zariya da Maiduguri, ba za a iya cewa kasar ta ci gajiyar kafa su ba.

LABARAI MASU NASABA

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

Ya kara da cewa, babban makasudin kafa cibiyoyin da kudaden jama’a shi ne bunkasa masana’antu, da rage bukatar musayar kudaden waje, da samar da fa’idoji masu yawa ga kasar nan.

Idu ya ce IDCs, musamman Cibiyoyin shiyyoyi hudu, sun cika da manyan injina don yada ilimin fasahar masana’antu da fasahar da za su yi tasiri matuka kan yunkurin kasar na samar da masana’antu.

Ya bayyana damuwarsa cewa, “A tsawon shekaru, kusan dukkanin IDCs, ma’aikata da kayan aiki a yi asarar su kuma wasu kayan aikin sun daina aiki.

“Duk da cewa gwamnatin tarayya ta mika wadannan cibiyoyi ga hukumar kula da masu kananan sana’o’i ta kasa (SMEDAN) tsawon wasu shekaru a yanzu, babu wani abin da aka yi gaba daya don gyara wadannan cibiyoyi a halin da ake ciki.

“Idan ba a duba wannan yanayin ba, kasar za ta ci gaba da rasa moriyar masana’antu, wanda hakan zai shafi yanayin rayuwar jama’a.”

Majalisa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Daure Mutum Biyu Shekara 24 Saboda Kashe Wani Dan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

MASU ALAKA

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir
Manyan Labarai

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima
Manyan Labarai

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Next Post
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

ADC: Hayatu-Deen Ya Fi Atiku Ƙwarewa Da Gogewa – Babachir

June 9, 2026
‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.