ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Ban Kori Emefiele A Matsayin Gwamnan CBN Ba – Buhari

by Sadiq
2 years ago
Buhari

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana dalilin da ya sa bai kori Godwin Emefiele daga mukamin gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) ba a lokacin da ya karbi mulki a 2015.

Idan za a tuna cewa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ne, ya nada Emefiele a matsayin gwamnan CBN bayan tsige Sanusi Lamido Sanusi a farkon shekarar 2014.

  • Juyin Mulki: Rufe Iyakar Nijeriya Da Nijar Ya Jefa Arewa Cikin Tsaka Mai Wuya – Aliero
  • Jiang Ying: Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya 

Daga baya Jonathan ya sha kaye a zaben shugaban kasa na 2015 a hannun Buhari.

ADVERTISEMENT

Bayan hawansa mulki a shekarar 2015, Buhari ya kori kusan dukkan masu rike da mukaman siyasa da suka yi aiki da gwamnatin Jonathan, sai dai ya bar Emefiele ya ci gaba da zama gwamnan CBN.

Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da kaddamar da littafin da tsohon mai ba shi shawara kan kafafen watsa labarai, Femi Adesina ya rubuta, mai sunan ‘Aiki Tare Da Buhari’ a ranar Talata.

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

Tsohon shugaban kasar ya ce tsarin sauya fasalin Naira da Emefiele ya bullo da shi ya taimaka wa kasar nan wajen gudanar da sahihin zabe a 2023.

“Ba da gangan aka bullo da karancin kudi don jefa ‘yan Nijeriya cikin wahala ba. Dimokuradiyya tana bai wa mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu hana su ba. Mutane sun fahimci abubuwan da suka zaba, kuma ba mu tilasta su ba.

“A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye a Jihar Katsina, amma kuma ta ci zaben gwamna. Watakila sun dauki abubuwa da sauki tun da farko saboda jihata ce, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki.

“Na samu Emefiele a ofis a lokacin da na zo, kuma ba ni da wata kwakkwarar hujja a kan sa game da aikata wani abu, don haka zai zama rashin adalci idan na kore shi.

“Idan kana son hukunta mutum dole ne ka samu hujja a kansa game da wani laifi da ya aikata,” in ji Buhari.

Wannan shi ne karon farko da Buhari ya ziyarci babban birnin tarayya, Abuja tun bayan sauka daga mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.