• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Ban Kori Emefiele A Matsayin Gwamnan CBN Ba – Buhari

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalilin Da Ya Sa Ban Kori Emefiele A Matsayin Gwamnan CBN Ba – Buhari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya bayyana dalilin da ya sa bai kori Godwin Emefiele daga mukamin gwamnan babban bankin Nijeriya (CBN) ba a lokacin da ya karbi mulki a 2015.

Idan za a tuna cewa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ne, ya nada Emefiele a matsayin gwamnan CBN bayan tsige Sanusi Lamido Sanusi a farkon shekarar 2014.

  • Juyin Mulki: Rufe Iyakar Nijeriya Da Nijar Ya Jefa Arewa Cikin Tsaka Mai Wuya – Aliero
  • Jiang Ying: Sin Tana Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya 

Daga baya Jonathan ya sha kaye a zaben shugaban kasa na 2015 a hannun Buhari.

Bayan hawansa mulki a shekarar 2015, Buhari ya kori kusan dukkan masu rike da mukaman siyasa da suka yi aiki da gwamnatin Jonathan, sai dai ya bar Emefiele ya ci gaba da zama gwamnan CBN.

Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da kaddamar da littafin da tsohon mai ba shi shawara kan kafafen watsa labarai, Femi Adesina ya rubuta, mai sunan ‘Aiki Tare Da Buhari’ a ranar Talata.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Tsohon shugaban kasar ya ce tsarin sauya fasalin Naira da Emefiele ya bullo da shi ya taimaka wa kasar nan wajen gudanar da sahihin zabe a 2023.

“Ba da gangan aka bullo da karancin kudi don jefa ‘yan Nijeriya cikin wahala ba. Dimokuradiyya tana bai wa mutane damar bayyana ra’ayinsu, kuma ba mu hana su ba. Mutane sun fahimci abubuwan da suka zaba, kuma ba mu tilasta su ba.

“A zaben shugaban kasa, APC ta sha kaye a Jihar Katsina, amma kuma ta ci zaben gwamna. Watakila sun dauki abubuwa da sauki tun da farko saboda jihata ce, kuma suna tunanin za su yi nasara cikin sauki.

“Na samu Emefiele a ofis a lokacin da na zo, kuma ba ni da wata kwakkwarar hujja a kan sa game da aikata wani abu, don haka zai zama rashin adalci idan na kore shi.

“Idan kana son hukunta mutum dole ne ka samu hujja a kansa game da wani laifi da ya aikata,” in ji Buhari.

Wannan shi ne karon farko da Buhari ya ziyarci babban birnin tarayya, Abuja tun bayan sauka daga mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariCBNEmefieleGwamnan BankiMulki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Juyin Mulki: Rufe Iyakar Nijeriya Da Nijar Ya Jefa Arewa Cikin Tsaka Mai Wuya – Aliero

Next Post

Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

4 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

7 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

9 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

15 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

1 day ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 days ago
Next Post
Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

Xi Ya Taya Felix Antoine Tshisekedi Murnar Lashe Zaben Shugaban Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.