• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jaridar Daily Trust Ba Ta Yi Mana Adalci Ba- Fadar Shugaban Kasa 

Fadar Shugaban Kasa Ta Soki Rahoton Jaridar Daily Trust

by Abubakar Abba
3 years ago
Daily Trust

Fadar Shugaban kasa ta mayar da martani kan wani rahoto da jaridar Daily Trust da ta wallafa a ranar Litinin game da kamun bakin ludayin gwamnatin shugaba Buhari.

Gundarin rahoton ya mayar da hankali ne kan ikirarin cewar tun hawa kan karagar mulkin APC mai mulki babu abin da ya sauya a Nijeriya.

  • Mataimaki: Gwamnonin APC Na Alfahari Da Zabin Tinubu – Bagudu
  • Na Matsu Mulkina Ya Kare Na Sauka – Buhari

Amma a martanin da fadar shugaban kasa ta yi a ranar Litinin ta hannun, Malam Garba Shehu, ta ce ba daidai bane hasashen rahoton da suka yi ba, musamman wajen fadakar da alummar kasar.

A cewar sanarwar rahoton cin fuska ne kai tsaye ga shirye-shiryen da gwamnatin Buhari ta kirkiro kamar na tsarin fallasa barayin gwamnati ga ‘yan Nijeriya, inda sanarwar ta kara da cewa, dole ne a jinjina wa gwamnatin kan irin kokarinta.

Sanarwar ta ce, marubutan sun yi gaskiya ganin yadda suka ce, a cikin rahoton ita ma Nijeriya kamar sauran takwarorinta kasashen duniya na fuskantar matsin tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

A cewar sanarwar, “A yau Nijeriya ta ci gaba fiye da yadda gwamnatin shugaba Buhari ya iske ta, mussaman wajen bunkasa tattalin arziki Nijeriya, kokarin magance kalubalen rashin tsaro da yakar cin hanci da rashawa, abin sai dai ace, Allah san barka.”

Sanarwar ta buga misali da da cewa, “A 2015 Boko Haram sun kwace wasu yankuna a Arewa Maso Gabas amma gwamnatin Buhari ta kwato su, haka a watan Maris dakarun soji sun aika da jagoran ISWAP zuwa barzahu ta hanyar luguden wuta da jiragen yaki da gwamnatin ta sayo daga Amurka.

“Gwamnatin Buhari a tarihin Nijeriya ita ce ta farko da ta wanzar da mafita kan rikicin manoma da Fulani da Makiyaya ta hanyar kafa tsarin inganta kiwo na zamani na kasa (NLTP), wanda tuni aka kakkafa guraren yin kiwo na zamani, inda wannan ya taimaka matuka wajen rage yawan rikice-rikicen a tsakaninsu.

“Ita kanta Daily Trust, ta amfana da canjin shugabancin da Buhari ya samar, musamman wajen sha’anin tsaro domin a 2015 kofar shiga harabar Jaridar Daily Trust cike take da shingle da jami’an tsaro don gujewa harin ‘yan ta’adda amma a cikin shekaru bakwai na shugaba Buhari sun cire shingen.

“Gwamnatin Buhari ta karbo dubban miliyoyin kudaden gwamnati da wasu ‘yan Nijeriya suka wawure suka kai ketare wadanda kuma ta yi amfani da su don inganta rayuwar ‘yan kasar tare da zuba wasu kai tsaye, wajen dakile yaduwar annobar Korona ta hanyar tallafa wa talakawa da gyaran wasu hanyoyi da aikin jirgin kasa da kuma inganta wutar Lantarki.

“Kokarin da gwamnatin ke ci gaba da yi na kara sanya wa ta na ci gaba da samun aminta daga gun abokan huldarta na waje musamman wajen yakar cin hanci da rashawa, inda gwamnatin ta kirkiro da tsarin tara kudade a asusu na bai daya tare da karfafa ofishin Akanta-Janar na kasa don sa ido kan yadda ake tafiyar da kudaden gwamnati

“Gwamnatin ta samu nasara wajen dora fannin tattalin arziki a kan turba musamman ta hanyar samar da tsare-tsare, haka ta yi kokari wajen kaucewa fadawar kasar a cikin barazar karancin abinci da ya tura wasu kasashe bango, gwamnatin ta kuma kafa shirin haramta shigo da shinkafa daga ketare, inda wannan ya ba ta damar adana Dalar abinci miliyan biyar.

“Mun samar da Dalar shinkafa da dama a wasu jihohin kamar su Kebbi, Abuja, Neja, Gombe da kuma jihar Ekiti”.

A cewar sanarwar, an kara samun kakkafa manyan masana’antun sarrafa Shinkafa 54 tare da kakkafa kanana 1,000 da kuma farafado da masana’antun sarrafa takin zamani 57, inda sanarwar ta kara da da cewa kimamin marasa karfi miliyan 20 ne suka amfana da tallafin kudade ta hanyar tura masu daga bankuna, gwamnatin ta kirkiro da ciyar da ‘yan makaranta da sauransu kafa shirin.

A kashe, sanarwar ta ce, a irin wannan yanayin da kasar ke tunkarar zabubbuka, suka mai zafi ga gwamnati ta siyasa da sharhin ya yi, musamman a kan gwamnatin Buhari abu ne da ba a yi wa gwamnatin adalci ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista
Labarai

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan – Malami

Gwamnatin Buhari Za Ta Yi Mai Yiwuwa Wajen Tabbatar Da Tsaro A Kasar Nan - Malami

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.