• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yawaitar Hadurran Mota A Hanyoyin Kasar Nan

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Yawaitar Hadurran Mota A Hanyoyin Kasar Nan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Munanan hadurran mota da suka auku a lokacin bukukuwan da suka gabata wani abu ne mai tayar da hankala da ya kamata hukumomin da da lamuran suka shafa su gaggauta daukar matakin kawo karshen sake aukuwar su.

Ko a makon jiya ‘yansanda a Jiha Imo sun sanar da mutuwar wasu iyalai mutum 8 da hadarin mota ya rutsa da su a shataletalen Amanwozuzu da ke karamar hukumar Ikeduru ta Jihar Imo.

  • NIS Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Kaddamar Da “Operation Tsaron Iyaka”
  • Ba Wanda Zai Iya Kawo Tsaiko Ga Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

A kwanaki ma, matafiya 9 sun mutu a Jihar Osun a yayin da wata babbar mota ta saki hanya ta afka wa mutane, hakanan kuma a Jihar Kaduna wasu mutane 4 sun mutu yayin da mutum 56 suka jikkata a wani mummunan hadarin.

Wadannan na daga cikin hadurra kalilan da suka faru na lokacin bukukuwan da suka gabata a watan Disamba, 2023.

A rahoto na baya-bayan nan da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayar ya nuna, ‘yan Nijeriya 24 ke mu-tuwa a kullum sakamakon hatsarin mota.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Lamarin kuma yana kara munana ne a lokutan bukukuwa kamar kirismeti da bikin murnar sabuwar she-kara a yayin da mutane da dama suke tafiye-tafiye.

A wani rahoton kuma da Hukumar Kiyaye Hadurran Kan Titi (FRSC) ta fitar a watan Agusta na shekarar 2023, ta bayyana cewa a tsakanin watan da aka bayar da rahoton, ‘yan Nijeriya 24 su ke rika mutuwa a kullum a tsakanin watan Janairu zuwa watan Yuni na shekarar 2023.

Jimillar mutanen da suka rasa rayukansu a cikin wata 6 na shekarar 2023, kamar yadda FRSC ta ruwaito sun kai mutum 4,387, wanda hakan ke nuna da cewa, mutum ne 731 suka mutu, mutum 24 kenan a kullum.

Kafin wannan rahoto na watan Agusta, Hukumar FRSC ta bayyana cewa a watan Afrilu mutum 1,349 suka mutu sakamakon hadarin mota a tsakanin 1 ga watan Janairu, 2023 zuwa ranar 12 ga watan Afrilu na 2023.

Rahoton na watan Afrilu ya kuma bayyana cewa, a tsakanin lokacin da ake magana an yi hadari 2,463, ta kuma kara bayyana cewa, motoci 3,965 masu dauke da mutum 16,102 suka yi hadarin a lokuta daban-daban inda a cikinsu mutum 1,349 suka rasa rayukansu yayin da mutum 7,744 suka ji raunuka daban-daban.

Jami’in wayar da kan al’umma na hukumar FRSC, Bisi Kazeem, ya lura da cewa, hadurran sun auku ne a jihohi 36 na tarayyar Nijeriya da kuma yankin babban birnin tarayyar Abuja, ya kuma ce, “Daga Janairu zuwa Yuni, mutum 4,387 sauka mutu sakamakon hadurran mota yayin da kuma mutum 14,108 suka ji raunuka daban-daban.”

Abin takaici shi ne yadda ake asarar rayukan al’umma a kullum, ba a dauki rayuwa da muhimmanci ba a Nijeriya, ana kashe mutane ta hanyar gangaci amma babu wanda ake kamawa da laifin wannan ta’asar.

Amma kuma hadurran motoci sun fi yawaita a lokutan bukukuwa saboda yadda mutane ke tururuwan ganin sun koma garuruwansu na asali don gudanar da bukukuwan, abin har ya zama jiki.

Duk da mastalar tsaro da ake fuskanta a sassan Nijeriya, al’umma sun gwammace su yi tafiya ta hanyoyionmu musamman ganin yadda kudaden sufurin jirgin sama ya yi tashin gwauron zabo, ta yadda ya fi karfin talakan Nijeriya.

Amma kuma wasu da dama na tsoron tafiya ta hanyoyinmu saboda yawaitar hatsurran da ake samu wanda kuma yakan ya fi tsanani a lokutan bukukuwa.

A matsayinmu na gidan jarida muna sane da dalilan da ke kara yawaitar hadurran a manyan hanyoyin kasar nan, wadanda suka hada da ko dai halin da hanyoyin ke ciki da kuma halin da motocin ke ciki ko kuma gangaci daga masu tukin.

Duk da cewa, wasu dalilan na taimakawa wajen afkuwar hadurra a hanyoyinmu amma matsalar rashin kyawun hanyoyinmu ne a kan gaba wajen haifar da hatsurra a kasar nan.

In ka duba Gabas, Arewa, kudu da yammancin kasar duk lamarin daya ne, hanyoyin sun lalace. Hanyoyin Nijeriya sun yi lalacewar da a wasu wuraren manyan ramuka masu zurfi ne suka mamaye su gaba daya.

Rashin ingancin motocin da ake amfani da su shi ma babbar matsala ne da ya kamata a kawo wa dauki. In an sa ido yadda ya kamata za a iya rage motocin da ba su da lafiyar da ta kamata a hau hanya don yin tafiye-tafiye da su.

Sa ido don gano motocin da suke da matsala da kuma tsaurara hanyoyin karbar lasisi na da muhim-manci. Haka kuma ya kamata a kara horas da jami’an kula da motoci tare da ba su karfin kawar da mo-tocin da suka karya doka daga hanyoyinmu.

Haka kuma dole direbobi su kula yayin da suke a kan hanya don kauce wa aukuwar hadari, su bi duk-kan dokokin hanya tare da mutunta sauran masu amfani da hanyar.

Akwai bukatar jami’an FRSC da jami’an ‘yansanda su tabbatar da hukunta masu karya dokokin hanya, kamar masu gudun wuce kima da wuce moto ba bi sa ka’ida ba.

A kan haka, wannan jaridar ke kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su dauki matakan kariya daga af-kuwar hadari a kan hanyoyinmu da matukar muhimmanci.

Ya kamata gwamnati ta jagoranci kawo karshen mace-mace da raunukan da ake ji a hanyoyinmu, lokaci ya yi da za a dauki kwakkwaran mataki, ‘yan Nijeriya sun cancanci samun hanyoyi ba tare da fargabar hadari ba a lokutan bukukuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abdilahi Ismail Abdilahi: Furucin Xi Jinping Ya Burge Ni Matuka

Next Post

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Related

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

3 hours ago
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
Manyan Labarai

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

20 hours ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

21 hours ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

1 day ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

1 day ago
Next Post
Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta’azzara A Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Kara Ta'azzara A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

’Yansanda Sun Kama Mutum 2 Da Bindigogi Da Alburusai A Filato

August 14, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

NAF Ta Kashe ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Wata 8 A Nijeriya

August 14, 2025
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

August 14, 2025
Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

August 14, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.