• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Aminta Da Ɗauke Babban Bankin Nijeriya Zuwa Legas Ba – Kungiyar Matasan Arewa

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Ba Za Mu Aminta Da Ɗauke Babban Bankin Nijeriya Zuwa Legas Ba – Kungiyar Matasan Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon makon nan ne haɗaɗɗiyar Ƙungiyar matasan Arewa, wacce ta haɗa ƙungiyoyi 16 daga sassan jihohin Arewacin ƙasar nan suka gudanar da wani taron manema labarai a Kaduna domin nuna rashin amincewarsu da shirin gwamnatin Tarayya na mayar da wasu muhimman sassan babban bankin Nijeriya, CBN daga Abuja zuwa Legas.

Taron, wanda ya gudana a ɗakin taro na Arewa House, Shugaban tawagar ƙungiyoyin, Malam Murtala Abubakar ne ya jagoranci zaman, inda ya bayyana cewa “A yau mun haɗa ku a nan ne domin mu nuna adawarmu da damuwarmu kan shawarar mayar da wasu muhimman sassa guda biyar na Babban Bankin Nijeriya (CBN) daga Abuja zuwa Legas.

  • Ana Tuhumar Sojoji 30 Kan Yunkurin Juyin Mulki A Saliyo
  • Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya – Gwamnati

“Da kuma batun mayar da hedikwatar hukumar kula da filayen jiragen sama ta tarayya (FAAN) da ma’aikatar sufurin jiragen sama ta tarayya ta yi daga Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya zuwa Legas.”

Murtala ya kara da cewa, “Mu, ƙungiyoyin matasan Arewacin Nijeriya, muna wakiltar murya da muradun miliyoyin matasa daga yankin Arewacin ƙasar nan, waɗanda wannan shawarar ta shafa. Mun yi imanin cewa ba kawai ayyukan rashin gaskiya ba ne, har ma da illa ga ci gaban tattalin arziki, zamantakewa da siyasa na yankin Arewa da ma ƙasar baki ɗaya.”

Da ya ke tsokaci game da sassan masu muhimmanci da Babban bankin zai ɗauke zuwa Legas, Malam Murtala cewa ya yi, “Muna tambayar dalilan da ya sa Babban Bankin ƙasa ɗaukar wannan mataki a kan muhimman sassanta biyar, waɗanda suka hada da sashen Kula da Harkokin Bankuna; Sashen Kula da Sauran Cibiyoyin Hada-hadar Kuɗi; Sashen Kula da Buƙatun Masu hulɗa da Bankuna; Sashen Tsarin Sarrafa Biyan Kuɗaɗe da Sashen Dokokin Hada-hadar Kuɗi.”

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Babban Bankin ya kawo hujjar ɗaukar wannan mataki komawa Legas, inda ya ce ya ɗauki wannan tsari ne domin rage cunkoso a babban ofishinsa da ke Abuja, wanda aka gina domin ma’aikata 3,000, amma yanzu yana da 4,000.

To, amma sai dai Matasan sun yi nuni da cewa, wannan dalili ba shi da ƙarfi, domin babban bankin zai iya faɗaɗa ofishin nasa a Abuja cikin sauƙi, ko kuma ya raba
ma’aikatan nasa zuwa wasu yankuna, maimakon ya tattara su a Legas.

Ƙorafi da koken matasan Arewar, ba a kan Babban Bankin kaɗai ya tsaya ba, sun kuma yi tir ga Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama ta Tarayya bisa matakin da ta ɗauka na mayar da hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama (FAAN) zuwa Legas, “Wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar ɗa’a ta tarayya da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya,” in ji matasan.

A ƙarshe, matasan sun jawo hankalin gwamnati da cewa, “Muna kira ga Gwamnatin tarayya ta janye waɗannan matakan da Babban Bankin ƙasa da Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama suka ɗauka cikin gaggawa, sannan ta dawo da martabar Abuja, Babban Birnin Tarayya.

An zabi Abuja ne a matsayin babban birnin ƙasar nan don zamowarta a tsaka-tsaki ga jinsunan da yankunan kasar. Har ila yau, Abuja tana taimaka wa wajen daidaitawa ga yankuna da sassa daban-daban na kasar nan.

Ƙungiyoyin da suka haɗu a wannan taro, sun haɗa da ‘Arewa Defense League, Association of Northern Nigerian Students, Arewa Youth for Development and National Unity, Arewa Young Women’s Rights Advocate Council, Northern Youth in Defense of Democracy, Arewa Radio and Television Commentators, Northern Youth Democratic Agenda Da kuma The Time is Now, the Time is Ours Association.’

Sauran sun haɗa da ‘Arewa Youth Advocate for Peace and Unity Initiative, Northeast Youth Artisans Association, Bauchi State Citizens Action for Chang, Youth Initiative for Good Governance, Coalition of Tiv Youth Organization, Matasan Arewa Ina Mafita Development Association, Toro Youth Circle da Northern Youth Coalition Forum.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNFAANTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Ba Da Umurni Kan Gobarar Da Ta Faru A Birnin Xinyu Na Lardin Jiangxi

Next Post

CMG Ya Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Hukumar Watsa Labaran Antigua Da Barbuda

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

7 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

12 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

13 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

14 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

15 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

16 hours ago
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Hukumar Watsa Labaran Antigua Da Barbuda

CMG Ya Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Hukumar Watsa Labaran Antigua Da Barbuda

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.