ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Za Mu Aminta Da Ɗauke Babban Bankin Nijeriya Zuwa Legas Ba – Kungiyar Matasan Arewa

by Sulaiman
3 years ago
Matasan Arewa

A farkon makon nan ne haɗaɗɗiyar Ƙungiyar matasan Arewa, wacce ta haɗa ƙungiyoyi 16 daga sassan jihohin Arewacin ƙasar nan suka gudanar da wani taron manema labarai a Kaduna domin nuna rashin amincewarsu da shirin gwamnatin Tarayya na mayar da wasu muhimman sassan babban bankin Nijeriya, CBN daga Abuja zuwa Legas.

Taron, wanda ya gudana a ɗakin taro na Arewa House, Shugaban tawagar ƙungiyoyin, Malam Murtala Abubakar ne ya jagoranci zaman, inda ya bayyana cewa “A yau mun haɗa ku a nan ne domin mu nuna adawarmu da damuwarmu kan shawarar mayar da wasu muhimman sassa guda biyar na Babban Bankin Nijeriya (CBN) daga Abuja zuwa Legas.

  • Ana Tuhumar Sojoji 30 Kan Yunkurin Juyin Mulki A Saliyo
  • Sudan: Aiwatar Da “Yarjejeniyar Jiddah” Za Ta Shimfida Zaman Lafiya – Gwamnati

“Da kuma batun mayar da hedikwatar hukumar kula da filayen jiragen sama ta tarayya (FAAN) da ma’aikatar sufurin jiragen sama ta tarayya ta yi daga Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya zuwa Legas.”

ADVERTISEMENT

Murtala ya kara da cewa, “Mu, ƙungiyoyin matasan Arewacin Nijeriya, muna wakiltar murya da muradun miliyoyin matasa daga yankin Arewacin ƙasar nan, waɗanda wannan shawarar ta shafa. Mun yi imanin cewa ba kawai ayyukan rashin gaskiya ba ne, har ma da illa ga ci gaban tattalin arziki, zamantakewa da siyasa na yankin Arewa da ma ƙasar baki ɗaya.”

Da ya ke tsokaci game da sassan masu muhimmanci da Babban bankin zai ɗauke zuwa Legas, Malam Murtala cewa ya yi, “Muna tambayar dalilan da ya sa Babban Bankin ƙasa ɗaukar wannan mataki a kan muhimman sassanta biyar, waɗanda suka hada da sashen Kula da Harkokin Bankuna; Sashen Kula da Sauran Cibiyoyin Hada-hadar Kuɗi; Sashen Kula da Buƙatun Masu hulɗa da Bankuna; Sashen Tsarin Sarrafa Biyan Kuɗaɗe da Sashen Dokokin Hada-hadar Kuɗi.”

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Babban Bankin ya kawo hujjar ɗaukar wannan mataki komawa Legas, inda ya ce ya ɗauki wannan tsari ne domin rage cunkoso a babban ofishinsa da ke Abuja, wanda aka gina domin ma’aikata 3,000, amma yanzu yana da 4,000.

To, amma sai dai Matasan sun yi nuni da cewa, wannan dalili ba shi da ƙarfi, domin babban bankin zai iya faɗaɗa ofishin nasa a Abuja cikin sauƙi, ko kuma ya raba
ma’aikatan nasa zuwa wasu yankuna, maimakon ya tattara su a Legas.

Ƙorafi da koken matasan Arewar, ba a kan Babban Bankin kaɗai ya tsaya ba, sun kuma yi tir ga Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama ta Tarayya bisa matakin da ta ɗauka na mayar da hedikwatar Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama (FAAN) zuwa Legas, “Wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar ɗa’a ta tarayya da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya,” in ji matasan.

A ƙarshe, matasan sun jawo hankalin gwamnati da cewa, “Muna kira ga Gwamnatin tarayya ta janye waɗannan matakan da Babban Bankin ƙasa da Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama suka ɗauka cikin gaggawa, sannan ta dawo da martabar Abuja, Babban Birnin Tarayya.

An zabi Abuja ne a matsayin babban birnin ƙasar nan don zamowarta a tsaka-tsaki ga jinsunan da yankunan kasar. Har ila yau, Abuja tana taimaka wa wajen daidaitawa ga yankuna da sassa daban-daban na kasar nan.

Ƙungiyoyin da suka haɗu a wannan taro, sun haɗa da ‘Arewa Defense League, Association of Northern Nigerian Students, Arewa Youth for Development and National Unity, Arewa Young Women’s Rights Advocate Council, Northern Youth in Defense of Democracy, Arewa Radio and Television Commentators, Northern Youth Democratic Agenda Da kuma The Time is Now, the Time is Ours Association.’

Sauran sun haɗa da ‘Arewa Youth Advocate for Peace and Unity Initiative, Northeast Youth Artisans Association, Bauchi State Citizens Action for Chang, Youth Initiative for Good Governance, Coalition of Tiv Youth Organization, Matasan Arewa Ina Mafita Development Association, Toro Youth Circle da Northern Youth Coalition Forum.

Matasan Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
CMG Ya Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Hukumar Watsa Labaran Antigua Da Barbuda

CMG Ya Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Hukumar Watsa Labaran Antigua Da Barbuda

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.