• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gaskiya Ba Ta Buya…

by CMG Hausa
3 years ago

Idan ba a manta ba, a shekarar 2021 da ta gabata ne, Amurka ta kira taron demokiradiya, amma tun kafin lokacin wasu masharhanta ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyi game da wannan taro da ma ma’anarsa.

Bisa kalamai da jami’an Amurka suka sha furtawa, wai manufar taron ita ce wai yin bita, game da nasarorin da Amurka da kawayenta suka cimma a fannin karewa, da aiwatar da salon mulkin dimokaradiyya.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

To amma abun tambaya a nan shi ne, wace nasara tsarin demokiradiyar yamma ya haifar ga ita kanta Amurka da ma duniya?
Amsar wannan tambaya a bayyane take.

Idan muka yi la’akari da yanayin da duniyarmu take ciki a yanzu na fuskantar kalubaloli masu tarin yawa, kama daga koma bayan tattalin arziki, zuwa yaduwar cutar numfashin ta COVID-19, da yadda wannan annoba ta karade kasashen duniya manya da kanana, ciki har da Amurka ita kanta, inda ta yi mummunar barna. A fili take cewa, Amurka ta gaza wajen shawo kan wannan matsala, da ma sauran kalubalolin dake addabar kasar a cikin gida. Don haka, tsarin ya gaza a dukkan fannoni.

Na baya-bayan shi ne, wani sakamakon bincike da kafar yada labaran BBC ta wallafa dake nuna cewa, Larabawa ma sun yanke kauna kan tsarin demokuradiyyar yammacin duniya, a kokarin samar da daidaiton tattalin arziki a yankin gabas ta tsakiya da arewacin Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Rahoton ya ce, sama da rabin mutane 23,000 da cibiyar sadarwa ta Arab Barometer ta zanta da su a fadin yankin, sun amince cewa, tattalin arziki ya yi rauni a karkashin tsarin demokuradiyya na kasashen yamma.

Ana kara fahimtar cewa, tsarin demokuradiyyar yammacin duniya, ba cikakken tsarin gwamnati ba ne, kuma ba zai iya taba gyara komai ba.

Abin da wadanda suka gudanar da bincike suka gani da idonsu a fadin yankin shi ne, mutane na fama da yunwa, mutane na bukatar buredi, mutane na nuna takaici da tsarin da suke amfani da shi.” Galibin wadanda aka zanta da su, ba sa tsammanin yanayin tattalin arzikin kasashensu zai inganta a cikin ’yan shekaru masu zuwa.

Haka kuma, an ga yadda Amurka ke dandana kudar tsadar rayuwa, baya ga yadda sassan ’yan kasar ke kokawa game da rasa damar fadin albarkacin baki, da uwa uba matsalar kare hakkin bil adama, ta yadda kawo yanzu sanadiyyar bazuwar cutar COVID-19 kadai, dubban daruruwan Amurkawa suka rasa rayukan su.

Masu fashin baki na cewa, duk tsarin jagorancin da ya gaza wajen sauke nauyin kare rayukan al’umma, suka kuma kasa daidaita matsalolin tattalin arziki, da na zamantakewar al’ummarsu yadda ya kamata, shin anya kuwa ya dace su rika ambaton ko da sunan tsarin ma?
A takaice dai, bai dace kasashen duniya dake da ’yanci su rika barin masu ragin tsarin demokiradiyar yamma su rika amfani da su, da sunan kare demokaradiyya, a rika haifar da rarrabuwar kawuna ba.

A maimakon haka, kamata ya yi a mayar da hankali ga hadin gwiwar dukkanin sassan, wajen warware kalubalolin bai daya dake addabar daukacin bil adama, kuma lokaci zai kara fayyace boyayyun manufofin Amurka game da batun tsarin demokiradiya har da kokarin kare shi.

Tsarin demokuradiyya na kasar Amurka, wani sakamako ne da kasar ta samu bisa gwajin da ta yi ita kadai a cikin gidanta, don haka ba dole ne ya dace da sauran kasashe ba.

Saboda haka, kasar Amurka ba ta da ikon yin babakere game da mizanin demokuradiyya, da fakewa da maganar demokuradiyya wajen neman kulla kawance tare da wasu kasashe, da neman ta da rikici a duniya. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki
Daga Birnin Sin

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
Next Post
Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.