ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

by Sani Anwar and Sulaiman
1 year ago
Daurarru

Biyo bayan rahoton baya-bayan nan, game da fursunoni 86,000 a Nijeriya, babban jami’in gudanarwa na kamfanin Moneda, wani kamfanin hada-hadar kudi, Ejike Egbuagu, ya kaddamar da gidauniyar Egbuagu, da nufin ‘yantar da fursunoni 1,000 da ake tsare da su; ba bisa ka’ida ba a dukkanin fadin Nijeriya.

Kaddamar da bikin, wanda ya yi daidai da cikar Egbuagu shekaru 40 da haihuwa, ya gudana ne a gidan Moneda da Lekki a Jihar Legas, wanda ya samu halartar kwararrun masana shari’a da dama da suka yi alkawarin tallafa wa wannan gidauniya.

  • Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane
  • Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Har zuwa ranar 28 ga watan Afrilun 2025, gidajen yarin Nijeriya na amfani da kashi 136.7 cikin 100, wanda ke nuni da cewa; akwai matukar cunkoso a wadannan gidaje na yari. Jimillar wadannan fursunoni, sun hada da wadanda aka yankewa hukunci da kuma wadanda ake tsare da su kafin yanke musu hukuncin.

ADVERTISEMENT

Bisa kididdigar baya-bayan nan da hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Nijeriya ta yi da kuma rahotanni daga kungiyoyin kare hakkunan shari’a, kashi 70 cikin 100 na fursunonin da ke gidajen yarin Nijeriya, na nan suna dakon shari’a, ma’ana ba a yanke musu hukunci ba. Yayin da kimanin yara 26,000, ke gidan yari ko kadai iyayensu sun haife su a can ko kuma ana tsare da su ba tare an tabbatar da laifin da suka aikata ba.

Da yake yin jawabi a wajen kaddamar da taron, Egbuagu ya bayyana cewa; gidauniyar ta fara mayar da hankali ne wajen kyautata jin dadin fursunonin tare kuma da kokarin ganin an sako wadanda ake tsare da su, ba bisa ka’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

“Gidauniyarmu ta farko da aka kafa a shekarar 1952, ta tallafa wa masu fasaha daban-daban na Afirka, ta hanyar ba su damar shiga kasuwannin duniya. Gidauniyar Egbuagu, wadda aka kaddamar a yau; za ta mayar da hankali ne wajen kula da ayyukan shari’a, domin taimaka wa ‘yan Nijeriyan da ake tsare da su ba bisa ka’ida ba,” in ji shi.

“Babban bangaren da za mu bai wa fifiko shi ne, na matasan fursunoni, masu basirar kirkire-kirkire. Muna so mu taimaka musu su yi amfani da kwarewarsu, domin samun damar rike kawunansu ko da kuwa a gidajen yarin ne. Kazalika, bincikenmu zai mayar da hankali kan shekaru da kuma yanayin daurin da aka yi musu.”

Dangane da batun hadin gwiwa kuwa, Egbuagu ya kara da cewa; “Mun shirya yin aiki tare da kungiyoyin lauyoyi, ciki har da masu yin aiki kyauta. Tuni dai, wasu daga cikin kamfanonin lauyoyi da dama suka yi alkawarin taimaka mana, yayin da wasu lauyoyin kuma suka sha alwashin yin aiki da mu kyauta, a wasu lokutan kuma za mu biya su; idan akwai bukatar hakan.

Ya kara da cewa, ‘yan Nijeriya su yi tsammanin fara cikakken wannan aiki na gidauniya nan da watan Yunin 2025.

“A yanzu haka, muna kokarin kammala yarjejeniya tare da abokan aikinmu tare kuma da gabatar da kawunanmu ga gidajen fursunonin da ayyana abubuwan da muke son aiwatarwa. Mafi yawan wadannan fursunoni, ba su da ko da fayel, don haka; a cikin tsarikan da muke da su, za mu samar musu da fayal-fayal tare kuma da rubuta dalilan da yasa bai kamata su ci gaba da kasancewa a wadannan wurare ba.

“Wannan aiki, ko shakka babu zai dauki kimanin kwana 90, bayan haka; za mu fara shiga tsakani tare kuma da sanar da kamfanoni masu zaman kansu.”

Wata babbar lauya, mai suna Zikora Okwor-Wewan, wadda ita ma ta halacci kaddamarwar, ta bayyana farin cikinta game da wannan shiri, “Na yi aiki da fursunonin da ke jiran shari’a da kuma wadanda aka daure a gidajen yari ba bisa ka’ida ba. Lokacin da na ji batun wannan gidauniya, na yi matukar murna tare da yanke shawarar kasancewa tare da ita. Haka zalika, taimakawa wajen ‘yantar da fursunoni kimanin 1,000, na daya daga cikin ayyukan da nake so tare kuma da sha’awar yi”, in ji ta.

Har ila yau, ya sake nanata wannan kididdiga: “Nijeriya na da fursunoni kimanin 80,000, amma kusan kashi 70 cikin 100, har yanzu suna nan suna jiran shari’a. Kazalika, kusan kimanin 26,000 daga cikinsu, kananan yara ne, wadanda ko dai wadanda aka kama ko kuma wadanda aka haifa a can. Wasunsu ma, ba su da ko da shaidar takardun haihuwa, wasu kuma sun makale ne kawai a cikin tsarin.

Fursunoni
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta
Fursunoni
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.