• Leadership Hausa
Sunday, August 14, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Gaskiya Ba Ta Buya…

by CMG Hausa
1 month ago
in Daga Birnin Sin
0
Gaskiya Ba Ta Buya…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan ba a manta ba, a shekarar 2021 da ta gabata ne, Amurka ta kira taron demokiradiya, amma tun kafin lokacin wasu masharhanta ke ta bayyana mabanbantan ra’ayoyi game da wannan taro da ma ma’anarsa.

Bisa kalamai da jami’an Amurka suka sha furtawa, wai manufar taron ita ce wai yin bita, game da nasarorin da Amurka da kawayenta suka cimma a fannin karewa, da aiwatar da salon mulkin dimokaradiyya.

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

To amma abun tambaya a nan shi ne, wace nasara tsarin demokiradiyar yamma ya haifar ga ita kanta Amurka da ma duniya?
Amsar wannan tambaya a bayyane take.

Idan muka yi la’akari da yanayin da duniyarmu take ciki a yanzu na fuskantar kalubaloli masu tarin yawa, kama daga koma bayan tattalin arziki, zuwa yaduwar cutar numfashin ta COVID-19, da yadda wannan annoba ta karade kasashen duniya manya da kanana, ciki har da Amurka ita kanta, inda ta yi mummunar barna. A fili take cewa, Amurka ta gaza wajen shawo kan wannan matsala, da ma sauran kalubalolin dake addabar kasar a cikin gida. Don haka, tsarin ya gaza a dukkan fannoni.

Na baya-bayan shi ne, wani sakamakon bincike da kafar yada labaran BBC ta wallafa dake nuna cewa, Larabawa ma sun yanke kauna kan tsarin demokuradiyyar yammacin duniya, a kokarin samar da daidaiton tattalin arziki a yankin gabas ta tsakiya da arewacin Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

Rahoton ya ce, sama da rabin mutane 23,000 da cibiyar sadarwa ta Arab Barometer ta zanta da su a fadin yankin, sun amince cewa, tattalin arziki ya yi rauni a karkashin tsarin demokuradiyya na kasashen yamma.

Ana kara fahimtar cewa, tsarin demokuradiyyar yammacin duniya, ba cikakken tsarin gwamnati ba ne, kuma ba zai iya taba gyara komai ba.

Abin da wadanda suka gudanar da bincike suka gani da idonsu a fadin yankin shi ne, mutane na fama da yunwa, mutane na bukatar buredi, mutane na nuna takaici da tsarin da suke amfani da shi.” Galibin wadanda aka zanta da su, ba sa tsammanin yanayin tattalin arzikin kasashensu zai inganta a cikin ’yan shekaru masu zuwa.

Haka kuma, an ga yadda Amurka ke dandana kudar tsadar rayuwa, baya ga yadda sassan ’yan kasar ke kokawa game da rasa damar fadin albarkacin baki, da uwa uba matsalar kare hakkin bil adama, ta yadda kawo yanzu sanadiyyar bazuwar cutar COVID-19 kadai, dubban daruruwan Amurkawa suka rasa rayukan su.

Masu fashin baki na cewa, duk tsarin jagorancin da ya gaza wajen sauke nauyin kare rayukan al’umma, suka kuma kasa daidaita matsalolin tattalin arziki, da na zamantakewar al’ummarsu yadda ya kamata, shin anya kuwa ya dace su rika ambaton ko da sunan tsarin ma?
A takaice dai, bai dace kasashen duniya dake da ’yanci su rika barin masu ragin tsarin demokiradiyar yamma su rika amfani da su, da sunan kare demokaradiyya, a rika haifar da rarrabuwar kawuna ba.

A maimakon haka, kamata ya yi a mayar da hankali ga hadin gwiwar dukkanin sassan, wajen warware kalubalolin bai daya dake addabar daukacin bil adama, kuma lokaci zai kara fayyace boyayyun manufofin Amurka game da batun tsarin demokiradiya har da kokarin kare shi.

Tsarin demokuradiyya na kasar Amurka, wani sakamako ne da kasar ta samu bisa gwajin da ta yi ita kadai a cikin gidanta, don haka ba dole ne ya dace da sauran kasashe ba.

Saboda haka, kasar Amurka ba ta da ikon yin babakere game da mizanin demokuradiyya, da fakewa da maganar demokuradiyya wajen neman kulla kawance tare da wasu kasashe, da neman ta da rikici a duniya. (Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Sun Cafke Fursunan Da Ya Tsere Daga Gidan Yarin Kuje A Ogun

Next Post

Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

Related

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

7 hours ago
Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

9 hours ago
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

11 hours ago
Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

12 hours ago
Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak
Daga Birnin Sin

Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

1 day ago
Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa

1 day ago
Next Post
Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

Mai Gadin Kabarin Manzon Allah SAW Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

August 13, 2022
EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

August 13, 2022
Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

August 13, 2022
Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

August 13, 2022
Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

August 13, 2022
Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

August 13, 2022
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

August 13, 2022
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

August 13, 2022
Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

August 13, 2022
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

August 13, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.