• Leadership Hausa
Sunday, August 14, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia

by CMG Hausa
1 month ago
in Daga Birnin Sin
0
Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Kasar Amurka A Indonesia
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken a gefen taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 a tsibirin Bali na kasar Indonesia.

Wang ya bayyana cewa, a halin yanzu, dangantakar dake tsakanin kasashen Sin da Amurka na cikin wani mawuyacin hali, wanda gwamnatin Amurka da ta shude ta haddasa, har ma tana kara fuskantar kalubale.

  • Wang Yi Ya Jaddada Bukatar Aiwatar Da Matakan Gudanar Da Cudanyar Sassa Daban Daban A Zahiri

Babban dalili kuma shi ne, kasar Amurka tana da matsala game da yadda take kallon kasar Sin, kuma manufofinta game da kasar Sin sun kauce daga hanyar da ta dace.

Wang Yi ya jaddada cewa, tun da kasar Amurka ta yi alkawarin ba za ta nemi sauya tsarin kasar Sin ba, ya kamata ta mutunta tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin da jama’ar kasar Sin suka zaba, kana ta daina neman bata suna da takalar tsarin siyasa da manufofin cikin gida da waje na kasar Sin.

Tun da Amurka ta yi alkawarin cewa, ba za ta nemi tayar da wani “sabon yakin cacar baka ba”, to, ya kamata ta yi watsi da wannan tunani kwata-kwata. Tun da Amurka ta yi alkawarin ba za ta goyi bayan ‘yancin kai na yankin Taiwan ba, ya kamata ta daina neman yin illa da jirkita manufar Sin daya tak a duniya, da kuma daina fakewa da batun yankin Taiwan domin kawo cikas ga shirin sake dinkuwar kasar Sin cikin lumana. Tun da Amurka ta yi alkawarin cewa, ba ta da niyar tayar da wani rikici da kasar Sin, kamata ya yi ta mutunta iko da cikakkun yankunan kasar Sin, ta daina tsoma baki a harkokin cikin gidanta, da kuma kaucewa cin mutuncin halastacciyar moriyar kasar Sin ta hanyar fakewa da batun kare hakkin dan Adam da tsarin demokuradiyya.

Labarai Masu Nasaba

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

Blinken ya gabatar da manufofin Amurka game da kasar Sin, yana mai cewa, Amurka ba ta neman tayar da wani sabon yaki cacar baka kan kasar Sin, ko sauya tsarin kasar Sin, da kalubalantar matsayin JKS, da yi wa kasar Sin kawanya, ko kuma goyon bayan ‘yancin kai na yankin Taiwan.

Amurka ta kuduri aniyar daidaita al’amurran da za su iya kawo cikas ga dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, kuma tana son yin hadin gwiwa tare da kasar Sin ba tare da wata rufa-rufa ba. (Ibrahim)

ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Ka Kula da Lafiyarka, Kwankwaso Ga Tinubu

Next Post

Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

Related

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

7 hours ago
Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanyawa Mataimakiyar Ministan Sufurin Kasar Lithuania Takunkumi

9 hours ago
An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 Na Birnin Beijing

10 hours ago
Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Mika Wasu Takardun Amincewa Da Yarjejeniyoyi Biyu Ga ILO

11 hours ago
Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak
Daga Birnin Sin

Kungiyar Kawance Ta Sin Da Niger Na Goyon Bayan Manufar Sin Daya Tak

1 day ago
Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Wang Wenbin: Duk Irin Sauyin Yanayi Sin Za Ta Wanzar Da Fadada Bude Kofa

1 day ago
Next Post
Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

Zabin Shettima A Matsayin Mataimakin Tinubu Mataki Ne Mafi Cancanta- In ji Zulum

LABARAI MASU NASABA

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

An Bukaci Al’umma Su Ci Gaba Da Gudanar Da Addu’o’in Neman Zaman Lafiya

August 13, 2022
EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

EFCC Ta Cafke Malaman Addini 2 Da Wasu 5 Kan Zargin Damfara A Yanar Gizo A Kwara

August 13, 2022
Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

Fiye Da Miliyan 326 Muka Biya Ma’aikata Da Suka Yi Ritaya A Shekarar Bara -Hukumar Fansho

August 13, 2022
Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

Ganduje Ya Nada Shugabannin Gudanarwa Da Mambobin Hukumar Shari’a

August 13, 2022
Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

Akwai Babban Aiki A Gaban Erik ten Hag A Man U

August 13, 2022
Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

Jakadan Kasar Sin Dake Nijar Ya Gana Da Tsohon Shugaban kasar

August 13, 2022
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

August 13, 2022
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

August 13, 2022
Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

August 13, 2022
Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

Fasa Aure Bayan Sa Rana: Laifin Iyaye Ne, Saurayi Ko Budurwa?

August 13, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.