• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su – Minista

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya ta ce tana aiki ba dare ba rana don magance matsalolin tsaro da ake fama da ita a halin yanzu, ta hanyar yaki da rashin tsaro zuwa matsugunan masu aikata laifuka a fadin kasar nan.

Ministan ya ce a cikin makon da ya gabata, an kawar da ‘yan fashi, masu garkuwa da mutane da kuma ‘yan bindiga da dama, ko kuma aka kama su.

  • Jami’an Tsaro Sun Kama Ɗan Bindigar Da Ake Zargi Da Kashe Nabeeha
  • Zaben Cike Gurbin Makera: ‘Yan Takara Sun Yi Wa Liman Mubaya’a

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a Mohammed Idris Malagi ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa a Abuja.

“Ba zai yiwu a yi watsi da gaskiya a wannann lokaci na kalubalen da muka samu kanmu a matsayinmu na al’umma: illar hauhawar farashin kayayyaki a kan kasafin kudin mutane da na gida, da kuma barazanar tsaro a sassan kasar nan.

“Amma wannan wani bangare ne na labarin. Kamar yadda muhimman matakai daban-daban da gwamnatin tarayyar Nijeriya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ke dauka na tunkarar duk wadannan kalubalen.
“Mun amince da aiki da kuma nauyin kulawar da Gwamnatin Tarayya ta rataya a wuyan kowane dan Najeriya, a tsakanin shekaru, jinsi, addini, kabila, da zamantakewa,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Kashe-kashen Filato
Ministan ya ce hukumomin tsaro na taka tsan-tsan wajen tunkarar matsalolin da suka sake kunno kai a Jihar Filato da sauran yankunan da ke fama da rikici a daidai lokacin da shugaba Tinubu ya yi alkawarin samar da zaman lafiya a duk fadin kasar.

Ya kuma ba da tabbacin cewa za a gurfanar da masu aikata kisan-kiyashi da tashe-tashen hankula a wasu sassan kasar nan a Filato.

“Hakika rikicin da ya sake kunno kai a Jihar Filato abin takaici ne matuka, kuma muna ba da tabbacin cewa duk wadanda suka haddasa tashin hankali a can da kuma ko’ina a fadin kasar nan, an gurfanar da su a gaban kuliya. Za a yi adalci, kuma za a maido da zaman lafiya a dukkan al’ummomin da abin ya shafa.

“Muna jinjina wa jiga-jigan jami’an tsaro da na leken asiri wadanda ba sa barin wani abu don tabbatar da cewa muna cikin koshin lafiya a gidajenmu da kan manyan tituna, kuma masu aikata laifuka ba su da sararin shakar numfashi,” in ji Ministan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Manzon Allah

Allah Ya Yi Rantsuwa Da Girman Darajar Manzon Allah S.A.W (1)

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.