• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kara Kaimin Sintiri A Arewa Maso Gabas Domin Dakile Karancin Kayan Abinci

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
NIS

ACG James Sunday (a tsakiya) da sauran kwanturololin jihohin arewa maso gabas a wurin taron kaddamar da shirin

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Kwanturola Janar mai kula da shiyya ta uku (Zone C) da ta hade yankin arewa maso gabas mai shalkwata a Bauchi, ACG James Sunday, ya bayar da umarnin kara kaimin sintirin tsaron iyakokin kasa domin dakile silalewa da kayan abinci.

Umarnin a karkashin shiri na musamman mai taken “Operation Tsaron Iyaka” zai tabbatar da cewa kayan abincin da aka fi amfani da shi a gida kamar shinkafa, wake, albasa, doya da sauransu, ba a bi ta barauniyar hanya da su zuwa wasu kasashen ba.

ACG James Sunday ya ce daukar matakin ya zama wajibi saboda yadda ‘yan kasa ke fuskantar karancin abinci wanda ya zama wajibi NIS ta bayar da gudunmawa domin shawo kan matsalar.

NIS

A wata sanarwar manema labarai da ya aike wa LEADERSHIP Hausa, ACG James ya ce hukumarsu bisa hadin gwiwa da Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa za ta kara sa ido wajen tabbatar da cewa ba a fice da kayan abinci a tireloli da sauran manyan motoci ba illa wanda magidanta suka saya kawai domin ciyar da iyalansu.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

  • Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Ya ce jami’ansu a karkashin Kwanturola Janar ta NIS, Caroline Wuraola Adepoju sun mike haikan wajen tabbatar da samun nasarar sintirin musamman yadda shugabarsu take kara musu kwarin gwiwa a kan su jajirce wajen nuna kishin kasa a bakin aiki.

Kwanturololin NIS da ke yankin arewa maso gabas za su yi aiki kafada da kafada da takwarorinsu na Bauchi, Gombe da Filato domin musanyar bayanan sirri a kan duk wasu kayayyakin abinci masu yawa da ake safara a yankunansu inda hakan zai taimaka gaya wajen hana masu silalewa da abinci daga kasar nan cin karensu babu babbaka.

NIS

“Wannan wani mataki ne mai muhimmanci da ya zama wajibi mu dauka a NIS da ke shiyya ta uku (Zone C) tare da manyan ofisoshin da ke karkashin shiyyar domin mu taimaka wa gwamnati wajen yaki da safarar abinci ba bisa ka’ida ba wadda yake janyo karancinsa da karin wahalhalu ga ‘yan kasa.

“Jami’anmu tare da hadin gwiwar sauran hukumomi za su yi kokarin bankado masu kunnen kashi da ke haddasa karancin abincin ta hanyar safararsa ba bisa ka’ida ba, mun kimtsa tsaf domin tabbatar da tsaron iyakokin kasa a yankunan da ke karkashin kulawar NIS a shiyya ta uku (Zone C),” in ji ACG James Sunday.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciArewaArewa MasoFasa KwauriNISnorth east GabasSafara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Ki Hada Biredin Shawarma A Gida

Next Post

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

2 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

3 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

5 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

6 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

8 hours ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

9 hours ago
Next Post
Mata marayu

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

LABARAI MASU NASABA

NIS

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Kwanciyar Aure

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

July 26, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

July 26, 2025
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

July 26, 2025
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.