• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kara Kaimin Sintiri A Arewa Maso Gabas Domin Dakile Karancin Kayan Abinci

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
NIS

ACG James Sunday (a tsakiya) da sauran kwanturololin jihohin arewa maso gabas a wurin taron kaddamar da shirin

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Kwanturola Janar mai kula da shiyya ta uku (Zone C) da ta hade yankin arewa maso gabas mai shalkwata a Bauchi, ACG James Sunday, ya bayar da umarnin kara kaimin sintirin tsaron iyakokin kasa domin dakile silalewa da kayan abinci.

Umarnin a karkashin shiri na musamman mai taken “Operation Tsaron Iyaka” zai tabbatar da cewa kayan abincin da aka fi amfani da shi a gida kamar shinkafa, wake, albasa, doya da sauransu, ba a bi ta barauniyar hanya da su zuwa wasu kasashen ba.

ACG James Sunday ya ce daukar matakin ya zama wajibi saboda yadda ‘yan kasa ke fuskantar karancin abinci wanda ya zama wajibi NIS ta bayar da gudunmawa domin shawo kan matsalar.

NIS

A wata sanarwar manema labarai da ya aike wa LEADERSHIP Hausa, ACG James ya ce hukumarsu bisa hadin gwiwa da Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa za ta kara sa ido wajen tabbatar da cewa ba a fice da kayan abinci a tireloli da sauran manyan motoci ba illa wanda magidanta suka saya kawai domin ciyar da iyalansu.

Labarai Masu Nasaba

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

  • Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Ya ce jami’ansu a karkashin Kwanturola Janar ta NIS, Caroline Wuraola Adepoju sun mike haikan wajen tabbatar da samun nasarar sintirin musamman yadda shugabarsu take kara musu kwarin gwiwa a kan su jajirce wajen nuna kishin kasa a bakin aiki.

Kwanturololin NIS da ke yankin arewa maso gabas za su yi aiki kafada da kafada da takwarorinsu na Bauchi, Gombe da Filato domin musanyar bayanan sirri a kan duk wasu kayayyakin abinci masu yawa da ake safara a yankunansu inda hakan zai taimaka gaya wajen hana masu silalewa da abinci daga kasar nan cin karensu babu babbaka.

NIS

“Wannan wani mataki ne mai muhimmanci da ya zama wajibi mu dauka a NIS da ke shiyya ta uku (Zone C) tare da manyan ofisoshin da ke karkashin shiyyar domin mu taimaka wa gwamnati wajen yaki da safarar abinci ba bisa ka’ida ba wadda yake janyo karancinsa da karin wahalhalu ga ‘yan kasa.

“Jami’anmu tare da hadin gwiwar sauran hukumomi za su yi kokarin bankado masu kunnen kashi da ke haddasa karancin abincin ta hanyar safararsa ba bisa ka’ida ba, mun kimtsa tsaf domin tabbatar da tsaron iyakokin kasa a yankunan da ke karkashin kulawar NIS a shiyya ta uku (Zone C),” in ji ACG James Sunday.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciArewaArewa MasoFasa KwauriNISnorth east GabasSafara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Za Ki Hada Biredin Shawarma A Gida

Next Post

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

Related

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

9 minutes ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

1 hour ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

6 hours ago
NIS
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

7 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Mata marayu

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
NIS

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.