ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kara Kaimin Sintiri A Arewa Maso Gabas Domin Dakile Karancin Kayan Abinci

by Leadership Hausa
3 years ago
NIS

ACG James Sunday (a tsakiya) da sauran kwanturololin jihohin arewa maso gabas a wurin taron kaddamar da shirin

Mataimakin Kwanturola Janar mai kula da shiyya ta uku (Zone C) da ta hade yankin arewa maso gabas mai shalkwata a Bauchi, ACG James Sunday, ya bayar da umarnin kara kaimin sintirin tsaron iyakokin kasa domin dakile silalewa da kayan abinci.

Umarnin a karkashin shiri na musamman mai taken “Operation Tsaron Iyaka” zai tabbatar da cewa kayan abincin da aka fi amfani da shi a gida kamar shinkafa, wake, albasa, doya da sauransu, ba a bi ta barauniyar hanya da su zuwa wasu kasashen ba.

ACG James Sunday ya ce daukar matakin ya zama wajibi saboda yadda ‘yan kasa ke fuskantar karancin abinci wanda ya zama wajibi NIS ta bayar da gudunmawa domin shawo kan matsalar.

ADVERTISEMENT

NIS

A wata sanarwar manema labarai da ya aike wa LEADERSHIP Hausa, ACG James ya ce hukumarsu bisa hadin gwiwa da Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa za ta kara sa ido wajen tabbatar da cewa ba a fice da kayan abinci a tireloli da sauran manyan motoci ba illa wanda magidanta suka saya kawai domin ciyar da iyalansu.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

  • Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

Ya ce jami’ansu a karkashin Kwanturola Janar ta NIS, Caroline Wuraola Adepoju sun mike haikan wajen tabbatar da samun nasarar sintirin musamman yadda shugabarsu take kara musu kwarin gwiwa a kan su jajirce wajen nuna kishin kasa a bakin aiki.

Kwanturololin NIS da ke yankin arewa maso gabas za su yi aiki kafada da kafada da takwarorinsu na Bauchi, Gombe da Filato domin musanyar bayanan sirri a kan duk wasu kayayyakin abinci masu yawa da ake safara a yankunansu inda hakan zai taimaka gaya wajen hana masu silalewa da abinci daga kasar nan cin karensu babu babbaka.

NIS

“Wannan wani mataki ne mai muhimmanci da ya zama wajibi mu dauka a NIS da ke shiyya ta uku (Zone C) tare da manyan ofisoshin da ke karkashin shiyyar domin mu taimaka wa gwamnati wajen yaki da safarar abinci ba bisa ka’ida ba wadda yake janyo karancinsa da karin wahalhalu ga ‘yan kasa.

“Jami’anmu tare da hadin gwiwar sauran hukumomi za su yi kokarin bankado masu kunnen kashi da ke haddasa karancin abincin ta hanyar safararsa ba bisa ka’ida ba, mun kimtsa tsaf domin tabbatar da tsaron iyakokin kasa a yankunan da ke karkashin kulawar NIS a shiyya ta uku (Zone C),” in ji ACG James Sunday.

 

NIS
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Mata marayu

Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.