• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutumin Da Ya Kashe Tsohuwa Ya Sayar Da Sassan Jikinta A Ogun

by Sabo Ahmad
3 years ago
tsohuwa

Ana zargin wani mutum mai suna Dauda Bello, mai kimanin shekara 54 da laifin kashe wata tsohuwa mai suna Misis Mesesi Adisa da sayar da sassan jikinta.

Majiyarmu ta shaida mana cewa, bayan kama wanda ake zargin, ranar 7, ga watan Yuli, ya tabbatar wa da ‘yansanda,yadda ya kashe wannan tsoho, ya kuma sayar da kafadunsa da kuma kafafunsa. Marigayiyar Misis Adisa ta bata bat ne jim kadan bayan fitowarta daga gida.

  • Za A Hukunta Duk Wanda Aka Kama Yana Amfani Da Lambar Motar ‘Yan Sanda

Bayan faruwar wannan lamari ‘yan’uwan marigayiyar sun kai rahoto ofishin ‘yansanda na Sabo/Ilupeju, daga baya kuma suka koma ofishin masu yaki da masu garkuwa da ke sashin binciken manyan laifuka.

SP Taiwo wanda ke gudanar da bincike kan wannan lamari, ya ce guri na karshe da marigayiyar ta je shi ne, gidan wanda ake zargi da ke yankin Olodo a Abeokuta ta Arewa cikin jihar Ogun.

Mai Magana da yawun rundunar ‘yansanda na jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi,ya ce an tsare wanda ake zargin a ofishin ‘yansanda, domin ci gaba da gudanar da bincike.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Binciken da muka fara, wanda ake zargin ya tabbatar da cewa, sun dade suna sayar da mutane. Ya kara da cewa shi ne ya kira marigayiyar zuwa gidansa, domin su tattauna kan kasuwancinsu na sayar da mutane, sai lokacin da suke gana wa a gidansa, ya fahimci cewa,ta zo da wasu kudi masu yawa.

Wannan ta sa, ya kai mata duka a ka da wani katon katako, wanda kuma nan take ta fadi kasa sumammiya, ganin cewa ta mutu, sai ya dauki gawar ya kai ta daji.

Oyeyemi ya ce, wanda ake zargin ya tabbatar da aikata laifin, bayan kashe matar ya kuma lalube ta, wanda ya samu naira 22,200 a wajenta, bayan wannan danyen aiki sai ya gudu.

Da ya yi tunanin zai samu kudi masu yawa a wajen wannan tsohuwa,amma sai ya ga babu kudin da yake tsammani.
A kaeshe, wanda aka kaman ya kai ‘yansanda dajin da ya binne gawar wannan mata, sannan kuma ya nuna wa ‘yansanda wasu sassan jikin matar da ya cire.

Kwamishinan ‘yansanda, Lanre Bankole, ya umarci a gaggauta gurfanar da wanda ake zargin gaban kotu, domin yi masa hukunci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.