• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hon. Abdulkadir Rahis Na Taka Rawa Wajen Wakilci Nagari Ga Al’umma

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
Abdulkadir Rahis
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hon. Abdulkadir Rahis na daya daga cikin ‘yan majalisa mafiya taka rawa wajen wakiltar al’ummarsu.

A baya dai matasa sun taka muhimmiyar rawar gani sosai a sassa daban – daban na ci gaban kasar. Kusan ma za a iya cewa su ne kan gaba wajen tafiyar da al’amuran kasar bayan samun ‘yancinta.

  • Kwankwaso Ya Zabi Fasto Mataimakinsa A Zaben 2023

Alal misali, shuwagabanni irin su Janar Murtala Muhammad da Janar Yakubu Gowon, sun shugabanci kasar suna matasa, duk da cewa shugabanci ne na gidan soja, amma kuma sun taka muhimmiyar rawar gani. Haka kuma ko a yau, akwai irin su Abdulkadir Rahis, wanda shi ma matashi ne.

Kimanin shekaru goma sha biyar (15) ke nan, da tsohon dan majalisar birnin Maiduguri mai suna Umara Kumalia, ya wakilci birnin a majalisar tarayya ba a sake samu dan majalisa da ya maimaita wannan kujerar ba, sai Abdulkadir Rahis; wanda yanzu haka yake shirin maimaita kujerar a karo na uku.

Wannan shi ne jadawalin ‘yan majalisun da suka yi wannan kujerar daga 1999 zuwa yau.
Umara Kumalia a karkashin jam’iyyar APP (All People’s Party), daga Mayu 1999 zuwa Mayu, 2003 Miladiyya.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Umara Kumalia karo na biyu a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2003 zuwa Mayu, 2007 Miladiyya. Mustapha Baba Shehuri a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2007 zuwa Mayu, 2011 Miladiyya.

Gujbawu Kyari a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2011 zuwa Mayu, 2015 Miladiyya. Abdulkadir Rahis a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2015 zuwa Mayu, 2019 Miladiyya. Abdulkadir Rahis karo na biyu a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2019 zuwa Mayu, 2023.

Abdulkadir Rahis karo na uku a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2023 zuwa Mayu, 2027 idan Allah ya nufa.
Wane ne Abdukadir Rahis (Kadiri)?
Sunansa Abdulkadir Rahis, ana masa lakabi da Kadiri. An haife shi a shekarar 1968 a cikin birnin Maiduguri. Ya halarci makarantar kimiyya da fasaha ta karamar hukumar Bama wacce ya kammala a shekarar 1989.

Kadiri ya shiga siyasa a shekarar 1990, inda ya zama kansila a unguwar Shehuri South. A shekarar 1997 aka zabe shi a matsayin ciyaman din unguwar Shehuri South a karkashin inuwar jam’iyyar UNDP. A 1999 ya zama ma’aji (Treasurer) na jam’iyyar APP na birnin Maiduguri. Saboda kwarewarsa da iya shugabancinsa, ya sa aka nada shi mai kula da aiyukan kasilolin (Superbisory councilor for work) na birnin Maiduguri daga 2001 zuwa 2003.

A shekarar 2009 aka sake nada shi a matsayin memba a kungiyar kwallon kafa ta Borno, wato El-kalemi Warriors. Bayan ya yi ritaya daga memban, sai ya zama ciyaman din kungiyar. A shekarar 2009 ya sake zama zababben shugaban matasan birnin Maiduguri har zuwa 2011.

A cikin shekarar 2011 gwamnan jihar Borno Kashim Shettima ya nada shi a matsayin mashahurci na musamman ga gwamnan, kafin daga baya ya zama shugaban rikon kwarya a komitini zantarwar na birnin Maiduguri a 2015.
A cikin shekarar 2015 ya zama zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar birnin Maiduguri a karkashin jam’iyyar APC, wanda har yanzu yake kan wannan matsayin.

Babban matakin yakar talauci da kuma jahilci shi ne ilimi, wannan ya sa Kadiri ya gina wasu karin ajujuwa a sama da makarantu goma sha hudu da ke birnin Maiduguri.
Bayan haka, yana dauke da nawin karatun matasa da dama a birnin Maiduguri, domin ba su ilimin da za su dogora da shi a nan gaba, saboda kiyaye su daga fada wa kungiyoyin ta’addacin irin su Boko Haram.

Kadiri ya dasa fanfunan ruwa tare da kafa tankunan ruwa na zamani masu aiki da hasken rana (Sola) a unguwannin cikin birnin Maiduguri da suka hada da: Bulabulin da Bolori I da Bolori II da Fezzan da Gwange I da Gwange II da Gwange III da Gamboru Liberary da Hausari/Zango da Limanti da Lamisula/Jabbamari da Maisandari da Mafoni da Shehuri Sourth da kuma Shehuri North.

Sannan kuma yana bawa ‘yan gudun hijiran da Boko Haram suka kora daga karuruwansu tallafi abinci da abin kashewa. Ya kuma samarwa da duban matasan a Maiduguri mashin mai taya uku (Keke napep) domin su tsaya da kafafuwansu ba tare da sun zauna zaman kashe wando ko jiran ganima daga gwamnati ba. Domin hakan ne kadai zai fitar da su daga takaicin rashin aikin yi da zaman kashe wando da ake fama da shi.

Muna fatan alheri tare da addu’ar Allah Ya saka masa da alheri ya kuma ba mu shuwagabani masu kishin mu kamar shi, Amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Kukan Dadi Suke Yi – Buhari 

Next Post

Kyandar Biri: Adadin Wadanda Suka Kamu Sun Haura 1,000

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

3 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

4 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

7 days ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
kyandar biri

Kyandar Biri: Adadin Wadanda Suka Kamu Sun Haura 1,000

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.