ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hon. Abdulkadir Rahis Na Taka Rawa Wajen Wakilci Nagari Ga Al’umma

by Muhammad Maitela
4 years ago
Abdulkadir Rahis

Hon. Abdulkadir Rahis na daya daga cikin ‘yan majalisa mafiya taka rawa wajen wakiltar al’ummarsu.

A baya dai matasa sun taka muhimmiyar rawar gani sosai a sassa daban – daban na ci gaban kasar. Kusan ma za a iya cewa su ne kan gaba wajen tafiyar da al’amuran kasar bayan samun ‘yancinta.

  • Kwankwaso Ya Zabi Fasto Mataimakinsa A Zaben 2023

Alal misali, shuwagabanni irin su Janar Murtala Muhammad da Janar Yakubu Gowon, sun shugabanci kasar suna matasa, duk da cewa shugabanci ne na gidan soja, amma kuma sun taka muhimmiyar rawar gani. Haka kuma ko a yau, akwai irin su Abdulkadir Rahis, wanda shi ma matashi ne.

ADVERTISEMENT

Kimanin shekaru goma sha biyar (15) ke nan, da tsohon dan majalisar birnin Maiduguri mai suna Umara Kumalia, ya wakilci birnin a majalisar tarayya ba a sake samu dan majalisa da ya maimaita wannan kujerar ba, sai Abdulkadir Rahis; wanda yanzu haka yake shirin maimaita kujerar a karo na uku.

Wannan shi ne jadawalin ‘yan majalisun da suka yi wannan kujerar daga 1999 zuwa yau.
Umara Kumalia a karkashin jam’iyyar APP (All People’s Party), daga Mayu 1999 zuwa Mayu, 2003 Miladiyya.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Umara Kumalia karo na biyu a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2003 zuwa Mayu, 2007 Miladiyya. Mustapha Baba Shehuri a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2007 zuwa Mayu, 2011 Miladiyya.

Gujbawu Kyari a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2011 zuwa Mayu, 2015 Miladiyya. Abdulkadir Rahis a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2015 zuwa Mayu, 2019 Miladiyya. Abdulkadir Rahis karo na biyu a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2019 zuwa Mayu, 2023.

Abdulkadir Rahis karo na uku a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2023 zuwa Mayu, 2027 idan Allah ya nufa.
Wane ne Abdukadir Rahis (Kadiri)?
Sunansa Abdulkadir Rahis, ana masa lakabi da Kadiri. An haife shi a shekarar 1968 a cikin birnin Maiduguri. Ya halarci makarantar kimiyya da fasaha ta karamar hukumar Bama wacce ya kammala a shekarar 1989.

Kadiri ya shiga siyasa a shekarar 1990, inda ya zama kansila a unguwar Shehuri South. A shekarar 1997 aka zabe shi a matsayin ciyaman din unguwar Shehuri South a karkashin inuwar jam’iyyar UNDP. A 1999 ya zama ma’aji (Treasurer) na jam’iyyar APP na birnin Maiduguri. Saboda kwarewarsa da iya shugabancinsa, ya sa aka nada shi mai kula da aiyukan kasilolin (Superbisory councilor for work) na birnin Maiduguri daga 2001 zuwa 2003.

A shekarar 2009 aka sake nada shi a matsayin memba a kungiyar kwallon kafa ta Borno, wato El-kalemi Warriors. Bayan ya yi ritaya daga memban, sai ya zama ciyaman din kungiyar. A shekarar 2009 ya sake zama zababben shugaban matasan birnin Maiduguri har zuwa 2011.

A cikin shekarar 2011 gwamnan jihar Borno Kashim Shettima ya nada shi a matsayin mashahurci na musamman ga gwamnan, kafin daga baya ya zama shugaban rikon kwarya a komitini zantarwar na birnin Maiduguri a 2015.
A cikin shekarar 2015 ya zama zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar birnin Maiduguri a karkashin jam’iyyar APC, wanda har yanzu yake kan wannan matsayin.

Babban matakin yakar talauci da kuma jahilci shi ne ilimi, wannan ya sa Kadiri ya gina wasu karin ajujuwa a sama da makarantu goma sha hudu da ke birnin Maiduguri.
Bayan haka, yana dauke da nawin karatun matasa da dama a birnin Maiduguri, domin ba su ilimin da za su dogora da shi a nan gaba, saboda kiyaye su daga fada wa kungiyoyin ta’addacin irin su Boko Haram.

Kadiri ya dasa fanfunan ruwa tare da kafa tankunan ruwa na zamani masu aiki da hasken rana (Sola) a unguwannin cikin birnin Maiduguri da suka hada da: Bulabulin da Bolori I da Bolori II da Fezzan da Gwange I da Gwange II da Gwange III da Gamboru Liberary da Hausari/Zango da Limanti da Lamisula/Jabbamari da Maisandari da Mafoni da Shehuri Sourth da kuma Shehuri North.

Sannan kuma yana bawa ‘yan gudun hijiran da Boko Haram suka kora daga karuruwansu tallafi abinci da abin kashewa. Ya kuma samarwa da duban matasan a Maiduguri mashin mai taya uku (Keke napep) domin su tsaya da kafafuwansu ba tare da sun zauna zaman kashe wando ko jiran ganima daga gwamnati ba. Domin hakan ne kadai zai fitar da su daga takaicin rashin aikin yi da zaman kashe wando da ake fama da shi.

Muna fatan alheri tare da addu’ar Allah Ya saka masa da alheri ya kuma ba mu shuwagabani masu kishin mu kamar shi, Amin.

Rahis
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
kyandar biri

Kyandar Biri: Adadin Wadanda Suka Kamu Sun Haura 1,000

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.