ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hon. Abdulkadir Rahis Na Taka Rawa Wajen Wakilci Nagari Ga Al’umma

by Muhammad Maitela
4 years ago
Abdulkadir Rahis

Hon. Abdulkadir Rahis na daya daga cikin ‘yan majalisa mafiya taka rawa wajen wakiltar al’ummarsu.

A baya dai matasa sun taka muhimmiyar rawar gani sosai a sassa daban – daban na ci gaban kasar. Kusan ma za a iya cewa su ne kan gaba wajen tafiyar da al’amuran kasar bayan samun ‘yancinta.

  • Kwankwaso Ya Zabi Fasto Mataimakinsa A Zaben 2023

Alal misali, shuwagabanni irin su Janar Murtala Muhammad da Janar Yakubu Gowon, sun shugabanci kasar suna matasa, duk da cewa shugabanci ne na gidan soja, amma kuma sun taka muhimmiyar rawar gani. Haka kuma ko a yau, akwai irin su Abdulkadir Rahis, wanda shi ma matashi ne.

ADVERTISEMENT

Kimanin shekaru goma sha biyar (15) ke nan, da tsohon dan majalisar birnin Maiduguri mai suna Umara Kumalia, ya wakilci birnin a majalisar tarayya ba a sake samu dan majalisa da ya maimaita wannan kujerar ba, sai Abdulkadir Rahis; wanda yanzu haka yake shirin maimaita kujerar a karo na uku.

Wannan shi ne jadawalin ‘yan majalisun da suka yi wannan kujerar daga 1999 zuwa yau.
Umara Kumalia a karkashin jam’iyyar APP (All People’s Party), daga Mayu 1999 zuwa Mayu, 2003 Miladiyya.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Umara Kumalia karo na biyu a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2003 zuwa Mayu, 2007 Miladiyya. Mustapha Baba Shehuri a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2007 zuwa Mayu, 2011 Miladiyya.

Gujbawu Kyari a karkashin jam’iyyar ANPP (All Nigeria People Party), daga Mayu, 2011 zuwa Mayu, 2015 Miladiyya. Abdulkadir Rahis a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2015 zuwa Mayu, 2019 Miladiyya. Abdulkadir Rahis karo na biyu a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2019 zuwa Mayu, 2023.

Abdulkadir Rahis karo na uku a karkashin jam’iyyar APC (All Progressibe Congress), daga Mayu, 2023 zuwa Mayu, 2027 idan Allah ya nufa.
Wane ne Abdukadir Rahis (Kadiri)?
Sunansa Abdulkadir Rahis, ana masa lakabi da Kadiri. An haife shi a shekarar 1968 a cikin birnin Maiduguri. Ya halarci makarantar kimiyya da fasaha ta karamar hukumar Bama wacce ya kammala a shekarar 1989.

Kadiri ya shiga siyasa a shekarar 1990, inda ya zama kansila a unguwar Shehuri South. A shekarar 1997 aka zabe shi a matsayin ciyaman din unguwar Shehuri South a karkashin inuwar jam’iyyar UNDP. A 1999 ya zama ma’aji (Treasurer) na jam’iyyar APP na birnin Maiduguri. Saboda kwarewarsa da iya shugabancinsa, ya sa aka nada shi mai kula da aiyukan kasilolin (Superbisory councilor for work) na birnin Maiduguri daga 2001 zuwa 2003.

A shekarar 2009 aka sake nada shi a matsayin memba a kungiyar kwallon kafa ta Borno, wato El-kalemi Warriors. Bayan ya yi ritaya daga memban, sai ya zama ciyaman din kungiyar. A shekarar 2009 ya sake zama zababben shugaban matasan birnin Maiduguri har zuwa 2011.

A cikin shekarar 2011 gwamnan jihar Borno Kashim Shettima ya nada shi a matsayin mashahurci na musamman ga gwamnan, kafin daga baya ya zama shugaban rikon kwarya a komitini zantarwar na birnin Maiduguri a 2015.
A cikin shekarar 2015 ya zama zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar birnin Maiduguri a karkashin jam’iyyar APC, wanda har yanzu yake kan wannan matsayin.

Babban matakin yakar talauci da kuma jahilci shi ne ilimi, wannan ya sa Kadiri ya gina wasu karin ajujuwa a sama da makarantu goma sha hudu da ke birnin Maiduguri.
Bayan haka, yana dauke da nawin karatun matasa da dama a birnin Maiduguri, domin ba su ilimin da za su dogora da shi a nan gaba, saboda kiyaye su daga fada wa kungiyoyin ta’addacin irin su Boko Haram.

Kadiri ya dasa fanfunan ruwa tare da kafa tankunan ruwa na zamani masu aiki da hasken rana (Sola) a unguwannin cikin birnin Maiduguri da suka hada da: Bulabulin da Bolori I da Bolori II da Fezzan da Gwange I da Gwange II da Gwange III da Gamboru Liberary da Hausari/Zango da Limanti da Lamisula/Jabbamari da Maisandari da Mafoni da Shehuri Sourth da kuma Shehuri North.

Sannan kuma yana bawa ‘yan gudun hijiran da Boko Haram suka kora daga karuruwansu tallafi abinci da abin kashewa. Ya kuma samarwa da duban matasan a Maiduguri mashin mai taya uku (Keke napep) domin su tsaya da kafafuwansu ba tare da sun zauna zaman kashe wando ko jiran ganima daga gwamnati ba. Domin hakan ne kadai zai fitar da su daga takaicin rashin aikin yi da zaman kashe wando da ake fama da shi.

Muna fatan alheri tare da addu’ar Allah Ya saka masa da alheri ya kuma ba mu shuwagabani masu kishin mu kamar shi, Amin.

Rahis
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
kyandar biri

Kyandar Biri: Adadin Wadanda Suka Kamu Sun Haura 1,000

LABARAI MASU NASABA

2027: Masana Sun Yi Gargaɗi Game Da Bangar Siyasa Da Kalaman Ɓatanci

2027: Masana Sun Yi Gargaɗi Game Da Bangar Siyasa Da Kalaman Ɓatanci

September 12, 2026
Kwamitin Sulhu Na MDD Ya Bayyana Damuwa Game Da Yadda Yanayin Hare-haren Ta’addanci Ke Sauyawa

Kwamitin Sulhu Na MDD Ya Bayyana Damuwa Game Da Yadda Yanayin Hare-haren Ta’addanci Ke Sauyawa

September 12, 2026
Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

September 12, 2026
Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

September 12, 2026
Gwamnatin Katsina

Abinda Kasafin Gwamna Raɗɗa Na Shekarar 2027 Ya Ƙunsa

September 12, 2026
Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

September 12, 2026
Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

September 12, 2026
Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.