• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (4)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Zakka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

….Ci gaba daga makon da ya gabata

A wannan makon za mu duba Sarki na 6 a jerin wadanda suka muki masarautar Hadejia.

6. Buhari bin Sambo, 1848-50 zuwa 1851-1863
Abubakar Buhari bin Muhammad Sambo Digimsa shine Sarkin Hadejia na 4 amma bayan shekaru na Jihadi,ya kuma kasance a zamanin mulkinsa ne lokacin da ba za a manta da shi bane musamman ma idan ana maganar tarihin Hadejia.Sambo ya mutu ne a shekarar 1848 kuma sai ta kasance a hannun Buhari, kafin rasuwar mahaifinsa sai abin ya kasance duk wani salon iya mulki an nuna ma sa su maimakon a nuna wa Ahamadu wanda shi Sambo yana ganin shi ne zai gaje shi bayan rasuwarsa.

Duk da yake Buhari ne ya zama Sarkin Hadejia a wata matsalar da aka samu amma amincewa da hawan gadon Sarautar shi daga Sakkwato ne aka samu amincewar hakan.Buhari bai dade da hawa gadon Sarauta ba sai aka kashe dan’uwansa, Nalara Sarkin Auyo,wanda wani al’amari ne da yaba mahukuntan Sakkwato wata dama da suke jira ta cire ta cire Buhari daga gadon Sarauta.

Hakanan ma a shekarar 1850 da yake ba a samu nasarar ta hanyar difilomasiyya ba sai Kalifanci ya ba Wazirin Sakkwato umarni tare da taimakon wasu dakaru daga Katagum domin a dora dan’uwan Buhari Ahmadu a matsayin sabon Sarkin masarautar Hadejia za ayi hakan ne amma idan an samu wata dama.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Daga karshe dai an nada Ahamadu a matsayin Sarkin Hadejia a shekarar 1850 sai kuma Buhari ya koma Machina wato irin al’amarin nan da idan aka fidda Sarkin daga Sarauta ba’a barinsa a garin sai a kai shi wani wuri kamar yadda aka yi ma marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na 1, zamanin jamhuriya ta farko aka kai shi Katagum shekaar 1950 lokacin da aka nada Ado Bayero matsayin sabon Sarkin Kano.Sai dai kuma wani al’amari na Allah cikin shekara daya ce kawai sai ga Buhari ya sake dawowa Hadejia inda ya fafata a shekarar 1851,bayan samun dakaru masu yawa da kuma kayan aiki wato Kudi ya fuskanci dakarun dan ‘uwansa Ahamadu duk kuwa da yake ya samu taimako daga Katagum, sai ga shi an samu galaba a kan dakarun shi aka kashe Ahamadu a fagen daga ba tare da wata wahala ba.Ta haka ne Buhari ya sake dawowa mulkin Hadejia a matsayin Sarkin ta duk da yake mahukunta na Sakkwato basu so,wannan shi ne mafarin maganar nan da ake yi mata lakabi da adawar Buhari ko abin nan da aka cewa (Taskar Suleiman Ginsau).

Sarkin Hadejia ya yi shekaru goma sha biyar yana matsayin kamar dan tawaye saboda ya cire masarautar Hadejia daga daular Usumaniyya da hedikwatarta ke Sakkwato.Abu daya da yake babbane shine yadda rashin biyayya ko goyon bayan Buhari ga daular Usumaniyya abin ya kara fitowa fili ne a wani artabu da aka yi a kauyen Kaffur.

 

A shekarar 1853 ce daular Usumaniyya ta sake daukatr wani mataki wanda take ganin zai iya kawo karshen wani Kallon masheka Ayar da ya ke yi mata, domin duk wadansu masarautun da ake yi ma kalon suna da kima an sa su a cikin yakin,amma daga karshe duk sai kidin nasu ya kare a jinjina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sashen Kera Batiran Lithium Na Kasar Sin Ya Bunkasa Da Kaso 25 Bisa Dari A Bara

Next Post

Firaministan Thailand: Cudanya Da Juna Bisa Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Raya Ci Gaban Shiyyoyi

Related

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

2 weeks ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

3 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

3 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

8 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

12 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

1 year ago
Next Post
Thailand

Firaministan Thailand: Cudanya Da Juna Bisa Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Raya Ci Gaban Shiyyoyi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.