• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafi: ‘Yan Kasuwa Dubu 10 Sun Samu Tallafin Dubu 50 Kowane A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Tallafi: ‘Yan Kasuwa Dubu 10 Sun Samu Tallafin Dubu 50 Kowane A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya cika alkawarin tallafawa masu kananan sana’o’i dubu 10, da Naira 50,000 kowanensu, da nufin bunkasa harkokin kasuwancinsu a sassan jihar.

Fintiri, ya bayyana haka a taro da masu kananan sana’o’in a dandalin taro na Mahmud Ribadu da ke Yola, ranar Juma’a.

  • Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100
  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Ya ce shirin na karfafawa da aka yi wa lakabin ‘yan kasuwan Fintiri’ muhimman ci gaba ne a yunkurin gwamnatoci na daukaka martabar zamantakewa da tattalin arzikin al’umma da ya hada duk bangarorin tattalin arziki.

M

Ya ci gaba da cewa “A matsayin gwamnati ta fahimci cewa kananan sana’o’i su ne kashin bayan al’ummomin yanki, da samar da sabbin abubuwa, samar da ayyukan yi, da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jama’a da jiha.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

“Shawarar raba wadannan kudade ya samo asali ne daga jajircewar da aka nuna na kawar da talauci da kuma bai wa ‘yan kasuwa damar bunkasa a kasuwannin hada-hadar kudade.

“Mun yi amanna ta hanyar bada taimakon kudi kai tsaye ga masu kananan kasuwanci dubu 10, muna da niyyar habaka kudirinsu, habaka ayyukansu, da ba su damar habaka ayyukansu zuwa ga samun ci gaba.

“Na fahimci kalubalen da masu kananan sana’o’i ke fuskanta, kama daga rashin isasshen jari zuwa karancin kayan aiki da ababen more rayuwa, da irin wadannan tallafin kudi ba kawai na hannu ba ne, a’a dabarun saka hannun jari a Jihar Adamawa,” in ji gwamnan.

Da yake magana kan mutanen da suka amfana da shirin, gwamna Umaru Fintiri, ya bukaci da su yi amfani da kudaden yadda ya kamata, ya ce su zuba jari a cikin sana’o’insu, tare da yin amfani da damar da ke gabansu, samar da kirkire-kirkire, kere-kere, da ya ce nasarar da su ka samu na da nasaba da ci gaban jihar.

Shi ma da yake jawabi, kwamishinan ma’aikatar bunkasa harkokin kasuwanci ta jihar, Honarabul James Iliya, ya ce shirin ‘yan kasuwan Fintiri ya taba duk wani lungu da sako na al’ummar jihar, ya yaba wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yi a yakin neman zabe.

Tun da farko da take jawabi shugabar hukumar PAWECA, Hajiya Aisha Bawa Bello, ta bayyana wadanda suka ci gajiyar shirin a matsayin ‘yan kasuwa, ta kuma yaba wa gwamnan bisa irin damar da ya ba su, da ba kasafai ake samu ba na yi wa al’umma hidima.

Ta ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin dubu 10 ne daga sassa 226 na jihar, ta kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnan ya samu tare da yin kira ga wadanda suka amfana da su mayar da hankali wajen sanin ya kamata da aiki tukuru.

Da ta ke magana a madadin wadanda su ka ci gajiyar shirin, Eunice Kiliyobas ta bayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya kuduri aniyar bai wa mabukata dama, ta ce za su yi amfani da tallafin bisa hanyar da ta dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adamawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100

Next Post

Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

6 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

8 hours ago
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

12 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

14 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

14 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

15 hours ago
Next Post
Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.