ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafi: ‘Yan Kasuwa Dubu 10 Sun Samu Tallafin Dubu 50 Kowane A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
Adamawa

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya cika alkawarin tallafawa masu kananan sana’o’i dubu 10, da Naira 50,000 kowanensu, da nufin bunkasa harkokin kasuwancinsu a sassan jihar.

Fintiri, ya bayyana haka a taro da masu kananan sana’o’in a dandalin taro na Mahmud Ribadu da ke Yola, ranar Juma’a.

  • Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100
  • Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Ya ce shirin na karfafawa da aka yi wa lakabin ‘yan kasuwan Fintiri’ muhimman ci gaba ne a yunkurin gwamnatoci na daukaka martabar zamantakewa da tattalin arzikin al’umma da ya hada duk bangarorin tattalin arziki.

ADVERTISEMENT

M

Ya ci gaba da cewa “A matsayin gwamnati ta fahimci cewa kananan sana’o’i su ne kashin bayan al’ummomin yanki, da samar da sabbin abubuwa, samar da ayyukan yi, da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jama’a da jiha.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

“Shawarar raba wadannan kudade ya samo asali ne daga jajircewar da aka nuna na kawar da talauci da kuma bai wa ‘yan kasuwa damar bunkasa a kasuwannin hada-hadar kudade.

“Mun yi amanna ta hanyar bada taimakon kudi kai tsaye ga masu kananan kasuwanci dubu 10, muna da niyyar habaka kudirinsu, habaka ayyukansu, da ba su damar habaka ayyukansu zuwa ga samun ci gaba.

“Na fahimci kalubalen da masu kananan sana’o’i ke fuskanta, kama daga rashin isasshen jari zuwa karancin kayan aiki da ababen more rayuwa, da irin wadannan tallafin kudi ba kawai na hannu ba ne, a’a dabarun saka hannun jari a Jihar Adamawa,” in ji gwamnan.

Da yake magana kan mutanen da suka amfana da shirin, gwamna Umaru Fintiri, ya bukaci da su yi amfani da kudaden yadda ya kamata, ya ce su zuba jari a cikin sana’o’insu, tare da yin amfani da damar da ke gabansu, samar da kirkire-kirkire, kere-kere, da ya ce nasarar da su ka samu na da nasaba da ci gaban jihar.

Shi ma da yake jawabi, kwamishinan ma’aikatar bunkasa harkokin kasuwanci ta jihar, Honarabul James Iliya, ya ce shirin ‘yan kasuwan Fintiri ya taba duk wani lungu da sako na al’ummar jihar, ya yaba wa gwamnan bisa cika alkawarin da ya yi a yakin neman zabe.

Tun da farko da take jawabi shugabar hukumar PAWECA, Hajiya Aisha Bawa Bello, ta bayyana wadanda suka ci gajiyar shirin a matsayin ‘yan kasuwa, ta kuma yaba wa gwamnan bisa irin damar da ya ba su, da ba kasafai ake samu ba na yi wa al’umma hidima.

Ta ce an zabo wadanda suka ci gajiyar tallafin dubu 10 ne daga sassa 226 na jihar, ta kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnan ya samu tare da yin kira ga wadanda suka amfana da su mayar da hankali wajen sanin ya kamata da aiki tukuru.

Da ta ke magana a madadin wadanda su ka ci gajiyar shirin, Eunice Kiliyobas ta bayyana gwamna Fintiri a matsayin wanda ya kuduri aniyar bai wa mabukata dama, ta ce za su yi amfani da tallafin bisa hanyar da ta dace.

Adamawa
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.