• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan baya, Isra’ila ta ci gaba da kaiwa zirin Gaza hare-hare, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka da dama. Amurka ce ta samar da da yawa daga cikin makaman da Isra’ila ta yi amfani da su. Bisa labarin da shafin yanar gizo na jaridar kasar Isra’ila wato Ha’aretz ya bayar, an ce, Amurka ta shafe tsawon watanni 5 tana jigilar makamai ta sama zuwa Isra’ila.

A wani bangare Amurka na tallafawa Isra’ila da makamai, yayin da a wani bangare na daban kuwa, ta yanke shawarar jefa wa fararen hula a Gaza abinci daga sama. Sai dai daga cikin dubban abincin da ta jefa, yawancinsu sun fada ne cikin teku, wadanda suka kasa biyan bukatun fararen hular Gaza da yawansu ya haura miliyan 2. Ban da wannan kuma, sakamakon yadda laimar sauka daga jirgin sama masu dauke da abincin sun gaza budewa cikin lokaci, ya sa abincin ya fada kai tsaye kan wasu gidaje da mutane dake kasa, abin da ya sa mutane 5 suka mutu.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Jamhuriyar Congo Tana Son Karfafa Zumunta Da Hadin Gwiwa Da Sin

Shin ko da gaske ne Amurka tana mai da hankali kan rikicin jin kai dake faruwa a Gaza?

Kungiyoyin jin kai da dama sun yi tir da hanyar da Amurka ta zaba ta samar da tallafin jin kai ta hanyar jefa abinci daga sama. A ganinsu, a maimakon bukatar kawarta wato Isra’ila da ta bude hanyoyin jin kai, ko daina samarwa Isra’ila makamai, Amurka ta zabi hanyar da ba ta dace ba, wato jefa abinci daga sama, kuma burin da take neman cimmawa shi ne samun goyon baya daga masu kada kuri’u a gida.

Ban da wannan kuma, shugaban kasar Amurka Joseph Biden ya sanar da shirin kafa wata tashar jirgin ruwa ta wucin gadi a gabar tekun bahar Rum dake Gaza, don baiwa yankin tallafin jin kai. Hakan ya jawo suka daga masu bibbiyar kafar sada zumunta ta X, wadanda suka yi zargin cewa, Amurka tana da karfin dakatar da rikicin da ake fuskanta a Gaza muddin ta daina samarwa Isra’ila makamai, amma ta yi wasan kwaikwayo na samar da tallafin jin kai.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Tallafin da Amurka ta bayar da kyar sun isa hannun fararen hula, amma makaman da ta samar sun halaka mutane masu dimbin yawa. ‘Yan siyasar Amurka su kan yi wasan kwaikwayo don samun kuri’u, amma a wannan karo masu gudun hijira ke yin asara, wadanda ba su da abinci ba su da gidaje kuma ba su da tsaro, ballantana hakkin Bil Adama. Shin ko ‘yan siyasar Amurka ba su jin kunya? (Mai zana da rubutu: MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaTallafi
ShareTweetSendShare
Previous Post

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 4

Next Post

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

Related

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
Ra'ayi Riga

Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a

5 days ago
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

1 week ago
Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya
Ra'ayi Riga

Ingancin Tattalin Arzikin Sin Mai Bude Kofa Na Bayyana Sosai Duba Da Yawan Zuwan Baki Masu Sayayya

1 week ago
Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
Ra'ayi Riga

Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho

2 weeks ago
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
Ra'ayi Riga

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

2 weeks ago
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

3 weeks ago
Next Post
Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.