• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Yi Alhinin Rasuwar Sheikh Maigano Da Ya Rasu A Saudiyya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Yi Alhinin Rasuwar Sheikh Maigano Da Ya Rasu A Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya nuna alhininsa da kaduwa bisa samun labarin rasuwar malamin addinin musulunci a jihar kuma daya daga cikin mambobin hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar, Sheikh Abdulrahman Umar Maigona da ya rasu a kasa mai tsarki ta Saudiyya. 

Sheikh Maigona ya rasu ne a ranar Alhamis a Makkah da ke kasar Saudiyya Arabiyya a matsayinsa mahajjaci.

  • 2023: INEC Za Ta Rufe Rajistar Katin Zabe A Karshen Watan Yuli
  • Tattalin Arzikin Kasar Sin Yana Kara Daidaita

A wata sanarwar da daraktan yada labarai na gidan gwamnatin jihar Gombe Malam Ismaila Uba Misilli ya fitar, gwamnan ya nuna matukar kaduwa da jijjiga bisa rasuwar malamin, ya misalta marigayi babban limamin masallacin Izalah mai lamba 8 a matsayin hazikin malami da ya yi rayuwa abin koyi kana ya kwashe tsawon shekaru yana koyar da ilimin addini da dora mutane bisa tafarkin Allah da sunnar Manzon (SAW).

Inuwa ya ce, rasuwar malamin babban gibi ne ba kawai ga zallar iyalansa ba har ma da illahirin jihar da kasar nan baki daya.

Daga nan sai gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai, al’ummar jihar Gombe, abokai ciki har da ministan sadarwa Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, hukumar gudanarwa da ma’aikatan Jami’ar jihar Gombe, inda marigayin yake a matsayin Malami a tsangayar da ilimin addinin musulunci tare da mika jaje ga illahirin al’ummar musulmai na jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Ya yi addu’ar Allah ya jikan marigayin ya gafarta masa dukkanin kura-kuransa kana ya sanya shi cikin Aljanna Madaukaka wato ‘Aljannat Firdaus’.

Idan za ku iya tunawa dai mun ba ku labarin da ke cewa Sheikh Abdur-Rahman Maigona, ya rasu ne a kasar Saudiyya sa’ilin da ke aikin hajjin bana a can.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeMalamiRasuwaSaudiyyaTa'aziyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kofin Zakarun Turai: Za A Wallafa Rahoton Abin Da Ya Faru A Wasan Karshe

Next Post

Bayan Daukar Rafinha, Barcelona Ta Taya Lewandowski

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

2 months ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

3 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

3 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

4 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

10 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

10 months ago
Next Post
Bayan Daukar Rafinha, Barcelona Ta Taya Lewandowski

Bayan Daukar Rafinha, Barcelona Ta Taya Lewandowski

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.