• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1

by Nuhu Ubale Ibrahim
1 year ago
in Bakon Marubuci, Fatawa, Ilimi
0
Goman Ƙarshe Na Watan Ramadan [Darajarsu Da Mutsayinsu] Na 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Goman ƙarshen Ramadan su ne mafi girman dararen duniya baki ɗaya, domin a cikinsu Lailatul-Ƙadari yake. Allah Ta’ala Yana cewa: “Lailatul-Ƙadari ya fi wata dubu alheri” Suratul Ƙadri aya ta 3.

Babban malamin tafsiri al-Imam al-Bagawi, Allah Ya yi masa rahama yana cewa: “Malaman tafsiri sun bayyana ma’anar ayar da cewa: aikata aikin ƙwarai a cikin daren Lailatul-Ƙadari shi ne ya fi alheri sama da aikin ƙwarai a cikin watanni dubu wanda babu Lailatul-Ƙadari a cikinsu”

  • CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1
  • SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

Hadisi ya tabbata a cikin Al-mujtaba na Imam an-Nasa’i da Musnad na Imam Ahmad daga Abu Huraira Allah Ya ƙara yarda a gare shi ya ce: Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ramadana ya zo muku, wata ne mai wata irin albrka, Allah Mai girma da ɗaukaka ya wajabta muku azumtar sa, ana buɗe ƙofofin Aljanna a cikinsa, ana kuma rufe ƙofofin Jahannama a cikinsa, a cikinsa akwai wani dare da ya fi wata dubu alheri, duk wanda aka haramta masa alherinsa, to, tabbas an haramta masa alheri”

Ya zo a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Duk wanda ya tsayu a daren Lailatul-Ƙadari yana mai imani da neman lada, to, an gafarta masa zunubansa”

Wannan dare yana cikin goman ƙarshe na Ramadan. Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana cewa da Sahabbai: Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a goman ƙarshe na Ramadan. Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Labarai Masu Nasaba

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Ana karɓo hadisi daga Nana Aishatu, Allah Ya ƙara yarda a gare ta, ta ce: Lalle Manzon Allah (S.A.W) ya ce: “Ku kirdadi Lailatul-Ƙadari a cikin dare mara na goman ƙarshe na Ramadana” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Manzon Allah (S.AW) ya fi kowa girman matsayi da alfarma da daraja da martaba a wurin Allah. Allah Ya gafarta masa abin da ya aikata da wanda bai aikata ba amma duk da haka yana ƙara ƙaimi da ƙwazo a goman ƙarshe na Ramadan sama da ƙwazonsa a goman farko da ta tsakiya na wannan wata mai albarka. Nana Aisha Allah Ya ƙara mata yarda ta ce: “Manzon Allah (S.A.W) ya kasance idan goman ƙarshe ta shiga, sai ya ƙara zage dantse, ya kuma raya daren gaba ɗaya, kuma ya tayar da iyalansa daga barci” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito. A wata ruwaya ta Muslim cewa ta yi:” Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana ƙoƙari a goman ƙarshe irin ƙoƙarin da baya yinsa a waninsa”

Sayyadina Aliyu ɗan Abu Ɗalib, Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: “Lalle annabi (S.A.W) ya kasance yana tayar da iyalansa a goman ƙarshe na Ramadana” Tirmizi ne ya ruwaito da salsala ingantacciya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 10 Karshe na RamadanAzumiLailatul KadriRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Ya Yi Da Kasashen Yamma Za Su Yi Watsi Da Tunanin Wai Sun Fi Sauran Kasashe

Next Post

Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Related

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

1 week ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

2 weeks ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

2 weeks ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

2 weeks ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

2 weeks ago
Next Post
Isra’ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

Isra'ila Ta Kori Kafar Talabijin Ta Al Jazeera Daga Kasarta

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.