• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samun Tunanin Kashin Kai Zai Tabbatar Da Damar Ci Gaba

by CGTN Hausa
1 year ago
Tunani

A shekarun baya bayan nan, kasar Amurka tana ta neman yin karin tasiri a nahiyar Afirka. Bisa wannan yunkuri, ana ta samun dimbin rahotanni daga kafofin yada labarai na kasashen yamma dake nuna wai “Amurka da Sin na takara da juna a nahiyar Afirka”, da “ kasashen yamma na takara da kasashen Sin da Rasha, da wasu kasashen dake gabas ta tsakiya, don kwatar damar kulla huldar kawance tare da kasashen Afirka”, da dai sauransu daga kafofin yada labarai na kasashen yamma. Hakan na sa mutum tsammanin cewa, watakila kasashen Afirka ba za su iya kaucewa daukar wani bangare, a tsakanin karfin dake takara da juna a duniya ba. Sai dai abun tambaya a nan shi ne ko kasashen na Afirka suna son yin haka?

Wata kila a ki yin zabi, ko ma a magance yarda da ra’ayin maida kasashen yamma cibiyar duniya, da neman dakile saura, zai fi dacewa ga kasashen Afirka, don neman biyan bukatunsu na kare moriyar kai.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Xi Jinping Ya Yi Shawarwari Tare Da Takwaransa Na Indonesia

A wajen taron musayar ra’ayi tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai karo na 3, da ya gudana a kwanan nan a birnin Beijing na Sin, masana da jami’ai na kasashen Afirka da na kasar Sin sun sake jaddada muhimmancin ra’ayin diplomasiyya na magance daukar wani bangare. Kana wannan ra’ayi ya zama daya da tunanin hadin gwiwar Sin da Afirka, wato maimakon nuna son kai da neman dakile saura, a bude kofa domin kowa ya iya halarta, da aiwatar da tunani na kasancewar dimbin bangarori masu fada a ji a duniya.

Taron na wannan karo ya kunshi dandalin tattaunawa guda 2, daya ya shafi musayar ra’ayi cikin daidaito, kan al’adu da tunani na Sin da Afirka. Daya kuwa ya shafi musayar ra’ayin raya kasa, don aza harsashin hadin gwiwar nan gaba. Kana babbar ma’anar taron ita ce, kamar yadda Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar tarayyar kasashen Afirka AU a kasar Sin ya fada, “Daidaita ra’ayi da magance bahaguwar fahimta, ta yadda za a karfafa fahimtar juna da girmama juna da hadin gwiwa, ta hanyar yin musayar ra’ayi”.

Nufinsa shi ne, ta hanyar tattaunawa, ake neman kawar da shingen tunani da ra’ayoyi marasa dacewa, da kasar Amurka da wasu kasashen dake yammacin duniya suka sanya wa kasashen Afirka da kasar Sin, da sauran kasashe masu tasowa. Ta yadda za a samu tunani na kai, da yiwuwar dogaro da kai, da samun ci gaban kasa mai dorewa.

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

Irin wannan cudanyar ra’ayi mai daraja, ta sa ana ta samun tunani masu muhimmanci a tarukan musayar ra’ayi, tsakanin Sin da Afirka ta fannin wayewar kai, da aka taba gudanarwa a baya.

Misali, Rahamtalla M. Osman, jakadan kungiyar kasashen Afirka AU a kasar Sin, ya taba bayyanawa a madadin kungiyar AU cewa, ya kamata a daina ta da rikici tsakanin mabambantan wayewar kai, da neman tabbatar da kasancewarsu tare, da daina ganin al’adun wasu sun fi na wasu, tare da karfafa cudanya, da koyi da juna tsakanin wayin kai daban daban.

Sa’an nan a nasa bangare, shugaban cibiyar nazarin manufofin kasashen Afirka na kasar Kenya Peter Kagwanja, ya taba bayyana cewa, “Aikin zamanantar da kasar Sin, da yadda ake neman zamanantar da kasashen Afirka sun bambanta, amma za a iya kaiwa ga cimma buri guda daya. Saboda haka, ci gaban kasar Sin ya karfafa gwiwar jama’ar kasashen Afirka. Mu ma muna son tabbatar da zamanantarwa bisa dogaro da karfin kanmu.”

Ban da haka, Charles Onunaiju, darektan cibiyar nazarin kasar Sin ta kasar Najeriya, ya taba bayyana cewa, babbar matsala da kasashen Afirka suke fama da ita, ita ce talauci. Kana babban dalilin da ya sa muke kokarin zamanantar da kanmu shi ne don biyan bukatun jama’a. A cewarsa, “ Ya kamata mu koyi dabarun da kasar Sin ta samu, a kokarinta na raya kai. Sa’an nan mu yi kokarin ganowa da daidaita muhimmin bangare dake bukatar a daidaita shi, yayin da muke neman raya tattalin arziki da zaman al’umma na kasashen Afirka. ”

Ta jawabansu za mu iya ganin cewa, jami’ai da masana na kasashen Afirka, sun fara dora karin muhimmanci kan kasancewar mabambantan wayewar kai tare (maimakon samun takara da rikici a tsakaninsu), da dogaro da kai a kokarin neman ci gaban kasa ( maimakon rungumar wai “daidaitaccen tsari” na kasashen yamma na tabbatar da ci gaba), da kokarin biyan bukatun jama’a (maimakon dora nauyi kan tsarin kasuwa mai ‘yanci), da sauran tunani, wadanda suka sha bamban da ra’ayoyin kasar Amurka, da na sauran kasashen yammacin duniya.

 

Hakan ba wani abun ban mamaki ba ne, saboda fasahohin da kasar Sin ta samu a kokarin raya kanta, sun nuna mana cewa, dole ne a samu tunani na kai, kafin a kai ga samun cikakken ‘yancin kai. Kana ya kamata a bi hanyar raya kasa ta musamman, da ta dace da yanayin da kasa ke ciki, har a kai ga samar da hakikanin ci gabanta. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Jirgin Sojoji Ɗauki Ya Kai Ba Luguden Wuta A Chikun Ba – Gwamnatin Kaduna

NAF Ta Kashe 'Yan Ta'adda Tare Da Tarwatsa Sansanoninsu A Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.