• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa a kan rashin saukar farashin kayayyaki, Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Zaman Lafiya da Wayar da Kai ta Kasa (NACOPEAM), Dakta Ahmad Saleh, ya bayyana hanyoyin da za a bi; don warware matsalar hauhuwar farashin kaya a Nijeriya.

Saleh ya bayyana abubuwan ne a shirin Barka Da Hantsi Nijeriya na Sashen Talabijin na Intanet na LEADERSHIP Hausa, da aka gabatar ranar Larabar da ta gabata.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo

Dakta Saleh, ya nunar da cewa matukar ana so a cimma burin haka, da farko ya kamata a kafa Hukumar Kayyade Farashi a Nijeriya.

“Idan ana so farashin kaya ya sauka a wannan kasa, wajibi ne a kafa wannan hukuma; wadda za ta yi aiki a lungu da sako na wannan kasa baki-daya.”

Kamar yadda Daktan ya bayyana a shirin, ya ce kafa wannan hukuma zai taimaka wajen kayyade farashin kayayyaki, inda ya bayar da misali da cewa ana sayar da Simintin Dangode a kan dubu shida da wani abu a Legas amma a Mambila Naira dubu tara ake sayarwa kuma a cikin kasa daya wanda haka bai kamata ba.

Labarai Masu Nasaba

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Haka zalika, dole ne wannan hukuma ta tabbatar da samar da farashin bai-daya a dukkanin kananan hukumomi 774 da muke da su a Nijeriya. “Wannan na daya daga cikin abubuwan da za su taimakawa wajen saukar farashin kayayyakin da ke ci wa ‘yan Nijeriya tiwo a kwarya a daidai wannan lokaci.” Ya bayyana.

Abu na biyu, kamar yadda Dr. Saleh ya bayyana shi ne, Bunkasa Masana’antun Cikin Gida: Bunkasa masana’antu zai taimaka kwarai da gaske wajen saukar farashin kayayyaki a cewar Masanin, domin kuwa a duk yayin da ya kasance abubuwan da ake shigowa da su; sun rinjayi wadanda ake fita da su, dole ne a fuskanci matsalar hauhawar farashin kaya.

Ya kara da cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen farfado da masana’antu tare da karfafa samar da abubuwan da za a rika fitar da su zuwa kasashen ketare, don sake farfado da tattalin arzikin wannan kasa, misali kamar bangaren harkar noma, ma’adanai da sauran makamantansu.

Domin kuwa, Nijeriya kasa ce da Allah ya azurta da dukkanin wani nau’i na arziki, wanda idan aka tsaya aka kyautata amfani da shi yadda ya kamata, za a samu kyautatuwar tattalin arziki da wadata da kuma jin dadi a kasar baki-daya.

Sai kuma na uku, da ya yi kiran a kafa Kotun Hukunta Duk Wanda Ya Bijire Wa Dokar Kasa: “Idan har ana so a cimma wannan manufa ta samun saukar farashin kayayyaki a fadin wannan kasa, ya zama wajibi ya kasance ana hukunta duk wanda ya ci karo da doka. Misali, a Kasar Ghana, lokacin da bankuna suka saba wa ka’idojin harkokin kudaden waje; ba tare da wani bata lokaci ba aka hukunta su”, in ji Daktan.

Don haka, ya zama dole Nijeriya ta mike tsaye wajen hukunta masu aikata laifuka, musamman ma wadanda aka samu da laifin cin hanci da rashawa, ya kasance ana yanke musu hukunci irin na babu sani; babu sabo. Dalili kuwa, babu abin da ya mayar da Nijeriya baya tare da dakile ci gabanta, kamar wannan dambarwa ta cin hanci da rashawa a wannan kasa, a cewar Dakta Sale.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarashiKayayyakiSauki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

Next Post

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Related

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

51 minutes ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

2 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

3 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

6 hours ago
Borno
Labarai

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

7 hours ago
Yajin aiki
Labarai

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

9 hours ago
Next Post
Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

LABARAI MASU NASABA

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

August 11, 2025
Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.