• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba komai ba ce illa rabin jikin PDP da ya rube, saboda kashi 80 na ‘ya`yan APC duk tsofaffin ‘yan PDP ne.

Sule Lamido ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da gidan talabijin na Arise a kwanan nan game da fagen siyasar Nijeriya.

  • Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150
  • Majalisar Dattawa Za Ta Kafa Dokar Kare Hakkin ‘Yan Aikatau A Nijeriya 

Da yake mayar da martini kan maganar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya yi a makon da ya gabata na cewa babu gurbi a kujerar shugabancin Nijeriya a 2027, Lamido ya ce magana ce kawai ta ‘yan siyasa, domin tsarin mulki ya bayar da damar gudanar da zabe duk bayan shekaru 4.

Lokacin da aka tambaye shi game da ziyarar gwamnonin arewa a Amurka kan batun tsaro, ya ce yana matukar girmama ofishinsu na gwamnoni, amma ko kadan bai dace su tafi har Amurka ba saboda tattauna matsalolin tsaron Nijeriya.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta zo kan karagar mulki ne ba tare da manufofi ba, amma lokacin da PDP ke kan karagar mulki akwai dimbin manufofin da suka tsara gudanarwa domin ci gaban Nijeriya. Don haka ba za a taba hada hada gwamnatin PDP da ta APC ba, domin akwai bambanci sosai.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Kazalika, Sule Lamido ya ce sun ga yadda majan APC ta kasance ga ‘yan Nijeriya, wanda shi ya sa bai amince da manufar yin majar jam’iyyu saboda karbar mulki ba kawai, “na fi kaunar majan da za ta zo da kaykkyawar manufar yi wa ‘yan Nijeriya aiki. A lokacin da APC ta kulla maja a 2014 da sauran jam’iyyu ba su da wata mafufa illa iyaka su amshi shugabanci, sannan lokacin da suka hau karagar mulki kuma, majan ba ta amfanar da ‘yan Nijeriya ba. Don haka dole ne idan har za a yi maja ya kasance an bayyana manufofin da ake son cimmawa ba don amsar mulki ba kadai.”

Tsohon gwamnan, ya jaddada cewa lallai jam’iyyar PDP za ta dawo cikin hayyacinta duk da irin rikicin shugabanci da ta tsinci kanta a ciki. Yana mai cewar jam’iyyar ta shiga rikici mai yawan gaske ne sakamakon yadda wasu ‘ya`yanta ke yi wa APC aiki don durkusar da ita.

Ya bayyana yadda wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke ficewa daga jam’iyyar da cewa hukuncin kotu ne ya haddasa lamarin, sannan kuma wasu na jin tsoron Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Badakalar Kudi (EFCC), inda hakan ke sa su komawa jam’iyyar APC domin su kubuta daga zunubansu, “kamar yadda tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adam Oshiomole ya taba fadar cewa, duk wanda ya shiga APC za a yafe masa zunubin da ya aikata ba.” In ji shi.

Dangane da sha’anin tsaro kuma, Sule Lamido ya ce akwai babbar matsala wajen magance tsaro a kasar nan, domin an samu gazawar shugabanci wanda kuma babban illa ce ga al’umma masu tasowa. Yana mai yin kiran a kara matsa kaimi don magance tsaro a kasar nan, da samun shugabanci nagari da zai hada kan matasa masu tasowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCPDPSule Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Masana’antu Na Kasar Sin Sun Raba Fasahohinsu A Majalisar Dinkin Duniya

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

1 day ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

4 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

4 weeks ago
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma'aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.