ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
ADC

An samu rarrabuwar kawuna a jam’iyyar ADC kan sahihancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark a yayin da wani tsagi na jam’iyyar ya nuna bai amince da shugabancin rikon kwaya ba a halin yanzu.

Wannan ya faru ne a lokacin da wani bangare na jam’iyyar da tsohon dan takarar gwamnan Jihar Gombe, Nafiu Bala yake jagoranta ya yi ikirarin cewa shugabancin rikon gwarya na Dabid Mark ba halastacce ba ne kuma ya saba wa kundin tsarin jam’iyyar.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman ga Bala kan al’amuran jama’a, Dakta Aminu Alhassan ya Sanya wa hannu, ya ce tsagin ADC ya jaddada cewa kawai mambobi na asali wanda su ne ya kamata a bai wa jagorancn jam’iyar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dangane da takardar murabus na Cif Ralph Nwosu, mun lura cewa wasu mutane, musamman Dabid Mark da abokansa, su ne suka yi kokarin bayyana ikirarinsu na jagorancin jam’iyyar, wanda hakan ya sab awa ka’idoji da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya shimfida.

“Da farko dai, yana da muhimmanci a fayyace cewa murabus din Ralph Nwosu ba ta haifar da yanayi mai kyau ba ga kowa da ke cikin ADC. Ma’ana, ta bude tattaunawa mai muhimmanci game da makomar jagorancinmu, tattaunawa da ya kamata a gudanar bisa tsarin da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya kafa.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“Tsarin mulkin ADC ta bayyana cewa duk wanda ke neman zama shugaban jam’iyyar, dole ne ya kasance mamba nagari na jam’iyya. Wannan shi ne muhimman bukata ta asali wadda ba za a iya yin watsi da ita ko kauce mata ta kowace hanya ba.

“A cewar tsarin mulkin ADC, hanyar da ta dace don cike gurbin jagoranci bayan tafiyar Cif Nwosu ita ce, ta hanyar taron kwamitin zartarwa na kasa.”

Tsaagin jam’iyyar ta sake tabbatar da cewa Alhaji Nafiu shi ne halastaccen shugabanta na kasa tare da kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da hadin kai.

Ya kuma bayyana kwarin giwa kan ikon hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na kiyaye ka’idojin kundin tsarin mulki da na dimokuradiyya a cikin harkokin jam’iyyar siyasa.

Ya kara da cewa, “Wannan taron zai zama dandalin tattaunawa kan hanyar ci gaba kuma za a biyo bayansa da tantancewa a matakai na gaba na taron jam’iyyar. Wannan ne inda za mu tabbatar da cewa jagorancin jam’iyyarmu an kayyade ta ne daga wadanda ke da gaske suna sha’awar ra’ayoyi da manufofin ADC.”

“Muna so mu jaddada cewa babu wani tanadi a cikin tsarin dokokin hukumar zabe da tsarin mulki ko dokokin jam’iyyar ADC da ke ba mutum damar karbar jagoranci ba tare da cika sharuddan zama mamba ba da tsarin dimokuradiyya ya tanada.

“Ayyukan da Dabid Mark da abokan huldarsa ke yi ba kawai saba wa tsarin mulkin jam’iyyarmu ba ne, yana kuma nuna rashin girmamawa ga ka’idojin dimokuradiyya da ADC ta tsayu a kai.

“Muna kira ga mambobinmu masu muhimmanci da jajircewa, ku da ku kasance cikin zaman lafiya da kuma mayar da hankali a wannan lokaci na neman samun sauye-sauye. Ci gaban da muka yi a matsayin jam’iya shaida ce ga aikin tukuru da jajircewar mambobinmu na asali.

“Dole ne mu kalubanci abubuwa marasa kyau na wadanda ke son kawo cikas ga hadin kanmu da ci gabanmu. ADC jam’iyya ce da aka gina bisa ginshikin gaskiya, hadin kai, da dabi’un dimokuradiyya, kuma dole ne mu yi aiki tare wajen kare wadannan ka’idoji.

“A daidai wannan lokaci, muna kuma son tabbatar da cewa muna da kwarin giwa kan hukumar zabe ta kasa wacce ba ta dogaro da gwamnati da shiga cikin wannan lamari. Muna yarda da sadaukarwarta wajen tabbatar da bin doka da tsari da tabbatar da cewa ana girmamawa kuma ana bin tsarin dimokuradiyya a cikin jam’iyyun siyasa. Jam’iyyar ADC ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da INEC don inganta yanayin siyasa wanda zai kasance mai kyau tare da martaba tsarin dimokuradiyya.

“A karshe, muna goyon bayan Alhaji Nafiu a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na gaskiya. Jagorancinsa zai zama mai mutunta ka’idojin jam’iyyarmu a wannan lokaci na canji, kuma muna da tabbacin cewa zai kula da hakkin asalin mambobinmu masu daraja. Muna kira ga dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar ADC na asali su goyi bayan Alhaji Nafiu da kuma aiki tare da shi don inganta jam’iyyarmu da al’umar da muke yi wa hidima.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

LABARAI MASU NASABA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Sana’ar Ɗinki: Yadda Telolin Zariya Suka Yi Fice A Sassan Afirka

July 10, 2026
Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

Shugaba Xi Ya Gana Da Firaministan Koriya Ta Arewa A Beijing

July 10, 2026
Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira

July 10, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.