ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
ADC

An samu rarrabuwar kawuna a jam’iyyar ADC kan sahihancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark a yayin da wani tsagi na jam’iyyar ya nuna bai amince da shugabancin rikon kwaya ba a halin yanzu.

Wannan ya faru ne a lokacin da wani bangare na jam’iyyar da tsohon dan takarar gwamnan Jihar Gombe, Nafiu Bala yake jagoranta ya yi ikirarin cewa shugabancin rikon gwarya na Dabid Mark ba halastacce ba ne kuma ya saba wa kundin tsarin jam’iyyar.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Gwamna Lawal Ya Ziyarci Yankunan Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Zamfara

A cikin wata sanarwa da mai ba da shawara na musamman ga Bala kan al’amuran jama’a, Dakta Aminu Alhassan ya Sanya wa hannu, ya ce tsagin ADC ya jaddada cewa kawai mambobi na asali wanda su ne ya kamata a bai wa jagorancn jam’iyar.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dangane da takardar murabus na Cif Ralph Nwosu, mun lura cewa wasu mutane, musamman Dabid Mark da abokansa, su ne suka yi kokarin bayyana ikirarinsu na jagorancin jam’iyyar, wanda hakan ya sab awa ka’idoji da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya shimfida.

“Da farko dai, yana da muhimmanci a fayyace cewa murabus din Ralph Nwosu ba ta haifar da yanayi mai kyau ba ga kowa da ke cikin ADC. Ma’ana, ta bude tattaunawa mai muhimmanci game da makomar jagorancinmu, tattaunawa da ya kamata a gudanar bisa tsarin da kundin tsarin mulkin jam’iyyarmu ya kafa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Tsarin mulkin ADC ta bayyana cewa duk wanda ke neman zama shugaban jam’iyyar, dole ne ya kasance mamba nagari na jam’iyya. Wannan shi ne muhimman bukata ta asali wadda ba za a iya yin watsi da ita ko kauce mata ta kowace hanya ba.

“A cewar tsarin mulkin ADC, hanyar da ta dace don cike gurbin jagoranci bayan tafiyar Cif Nwosu ita ce, ta hanyar taron kwamitin zartarwa na kasa.”

Tsaagin jam’iyyar ta sake tabbatar da cewa Alhaji Nafiu shi ne halastaccen shugabanta na kasa tare da kira ga ‘ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da hadin kai.

Ya kuma bayyana kwarin giwa kan ikon hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) na kiyaye ka’idojin kundin tsarin mulki da na dimokuradiyya a cikin harkokin jam’iyyar siyasa.

Ya kara da cewa, “Wannan taron zai zama dandalin tattaunawa kan hanyar ci gaba kuma za a biyo bayansa da tantancewa a matakai na gaba na taron jam’iyyar. Wannan ne inda za mu tabbatar da cewa jagorancin jam’iyyarmu an kayyade ta ne daga wadanda ke da gaske suna sha’awar ra’ayoyi da manufofin ADC.”

“Muna so mu jaddada cewa babu wani tanadi a cikin tsarin dokokin hukumar zabe da tsarin mulki ko dokokin jam’iyyar ADC da ke ba mutum damar karbar jagoranci ba tare da cika sharuddan zama mamba ba da tsarin dimokuradiyya ya tanada.

“Ayyukan da Dabid Mark da abokan huldarsa ke yi ba kawai saba wa tsarin mulkin jam’iyyarmu ba ne, yana kuma nuna rashin girmamawa ga ka’idojin dimokuradiyya da ADC ta tsayu a kai.

“Muna kira ga mambobinmu masu muhimmanci da jajircewa, ku da ku kasance cikin zaman lafiya da kuma mayar da hankali a wannan lokaci na neman samun sauye-sauye. Ci gaban da muka yi a matsayin jam’iya shaida ce ga aikin tukuru da jajircewar mambobinmu na asali.

“Dole ne mu kalubanci abubuwa marasa kyau na wadanda ke son kawo cikas ga hadin kanmu da ci gabanmu. ADC jam’iyya ce da aka gina bisa ginshikin gaskiya, hadin kai, da dabi’un dimokuradiyya, kuma dole ne mu yi aiki tare wajen kare wadannan ka’idoji.

“A daidai wannan lokaci, muna kuma son tabbatar da cewa muna da kwarin giwa kan hukumar zabe ta kasa wacce ba ta dogaro da gwamnati da shiga cikin wannan lamari. Muna yarda da sadaukarwarta wajen tabbatar da bin doka da tsari da tabbatar da cewa ana girmamawa kuma ana bin tsarin dimokuradiyya a cikin jam’iyyun siyasa. Jam’iyyar ADC ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da INEC don inganta yanayin siyasa wanda zai kasance mai kyau tare da martaba tsarin dimokuradiyya.

“A karshe, muna goyon bayan Alhaji Nafiu a matsayin shugaban jam’iyyar ADC na gaskiya. Jagorancinsa zai zama mai mutunta ka’idojin jam’iyyarmu a wannan lokaci na canji, kuma muna da tabbacin cewa zai kula da hakkin asalin mambobinmu masu daraja. Muna kira ga dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar ADC na asali su goyi bayan Alhaji Nafiu da kuma aiki tare da shi don inganta jam’iyyarmu da al’umar da muke yi wa hidima.”

ADC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.