ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba komai ba ce illa rabin jikin PDP da ya rube, saboda kashi 80 na ‘ya`yan APC duk tsofaffin ‘yan PDP ne.

Sule Lamido ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da gidan talabijin na Arise a kwanan nan game da fagen siyasar Nijeriya.

  • Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150
  • Majalisar Dattawa Za Ta Kafa Dokar Kare Hakkin ‘Yan Aikatau A Nijeriya 

Da yake mayar da martini kan maganar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya yi a makon da ya gabata na cewa babu gurbi a kujerar shugabancin Nijeriya a 2027, Lamido ya ce magana ce kawai ta ‘yan siyasa, domin tsarin mulki ya bayar da damar gudanar da zabe duk bayan shekaru 4.

ADVERTISEMENT

Lokacin da aka tambaye shi game da ziyarar gwamnonin arewa a Amurka kan batun tsaro, ya ce yana matukar girmama ofishinsu na gwamnoni, amma ko kadan bai dace su tafi har Amurka ba saboda tattauna matsalolin tsaron Nijeriya.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta zo kan karagar mulki ne ba tare da manufofi ba, amma lokacin da PDP ke kan karagar mulki akwai dimbin manufofin da suka tsara gudanarwa domin ci gaban Nijeriya. Don haka ba za a taba hada hada gwamnatin PDP da ta APC ba, domin akwai bambanci sosai.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Kazalika, Sule Lamido ya ce sun ga yadda majan APC ta kasance ga ‘yan Nijeriya, wanda shi ya sa bai amince da manufar yin majar jam’iyyu saboda karbar mulki ba kawai, “na fi kaunar majan da za ta zo da kaykkyawar manufar yi wa ‘yan Nijeriya aiki. A lokacin da APC ta kulla maja a 2014 da sauran jam’iyyu ba su da wata mafufa illa iyaka su amshi shugabanci, sannan lokacin da suka hau karagar mulki kuma, majan ba ta amfanar da ‘yan Nijeriya ba. Don haka dole ne idan har za a yi maja ya kasance an bayyana manufofin da ake son cimmawa ba don amsar mulki ba kadai.”

Tsohon gwamnan, ya jaddada cewa lallai jam’iyyar PDP za ta dawo cikin hayyacinta duk da irin rikicin shugabanci da ta tsinci kanta a ciki. Yana mai cewar jam’iyyar ta shiga rikici mai yawan gaske ne sakamakon yadda wasu ‘ya`yanta ke yi wa APC aiki don durkusar da ita.

Ya bayyana yadda wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke ficewa daga jam’iyyar da cewa hukuncin kotu ne ya haddasa lamarin, sannan kuma wasu na jin tsoron Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Badakalar Kudi (EFCC), inda hakan ke sa su komawa jam’iyyar APC domin su kubuta daga zunubansu, “kamar yadda tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adam Oshiomole ya taba fadar cewa, duk wanda ya shiga APC za a yafe masa zunubin da ya aikata ba.” In ji shi.

Dangane da sha’anin tsaro kuma, Sule Lamido ya ce akwai babbar matsala wajen magance tsaro a kasar nan, domin an samu gazawar shugabanci wanda kuma babban illa ce ga al’umma masu tasowa. Yana mai yin kiran a kara matsa kaimi don magance tsaro a kasar nan, da samun shugabanci nagari da zai hada kan matasa masu tasowa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma'aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.