ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba komai ba ce illa rabin jikin PDP da ya rube, saboda kashi 80 na ‘ya`yan APC duk tsofaffin ‘yan PDP ne.

Sule Lamido ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da gidan talabijin na Arise a kwanan nan game da fagen siyasar Nijeriya.

  • Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150
  • Majalisar Dattawa Za Ta Kafa Dokar Kare Hakkin ‘Yan Aikatau A Nijeriya 

Da yake mayar da martini kan maganar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya yi a makon da ya gabata na cewa babu gurbi a kujerar shugabancin Nijeriya a 2027, Lamido ya ce magana ce kawai ta ‘yan siyasa, domin tsarin mulki ya bayar da damar gudanar da zabe duk bayan shekaru 4.

ADVERTISEMENT

Lokacin da aka tambaye shi game da ziyarar gwamnonin arewa a Amurka kan batun tsaro, ya ce yana matukar girmama ofishinsu na gwamnoni, amma ko kadan bai dace su tafi har Amurka ba saboda tattauna matsalolin tsaron Nijeriya.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta zo kan karagar mulki ne ba tare da manufofi ba, amma lokacin da PDP ke kan karagar mulki akwai dimbin manufofin da suka tsara gudanarwa domin ci gaban Nijeriya. Don haka ba za a taba hada hada gwamnatin PDP da ta APC ba, domin akwai bambanci sosai.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Kazalika, Sule Lamido ya ce sun ga yadda majan APC ta kasance ga ‘yan Nijeriya, wanda shi ya sa bai amince da manufar yin majar jam’iyyu saboda karbar mulki ba kawai, “na fi kaunar majan da za ta zo da kaykkyawar manufar yi wa ‘yan Nijeriya aiki. A lokacin da APC ta kulla maja a 2014 da sauran jam’iyyu ba su da wata mafufa illa iyaka su amshi shugabanci, sannan lokacin da suka hau karagar mulki kuma, majan ba ta amfanar da ‘yan Nijeriya ba. Don haka dole ne idan har za a yi maja ya kasance an bayyana manufofin da ake son cimmawa ba don amsar mulki ba kadai.”

Tsohon gwamnan, ya jaddada cewa lallai jam’iyyar PDP za ta dawo cikin hayyacinta duk da irin rikicin shugabanci da ta tsinci kanta a ciki. Yana mai cewar jam’iyyar ta shiga rikici mai yawan gaske ne sakamakon yadda wasu ‘ya`yanta ke yi wa APC aiki don durkusar da ita.

Ya bayyana yadda wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke ficewa daga jam’iyyar da cewa hukuncin kotu ne ya haddasa lamarin, sannan kuma wasu na jin tsoron Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Badakalar Kudi (EFCC), inda hakan ke sa su komawa jam’iyyar APC domin su kubuta daga zunubansu, “kamar yadda tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adam Oshiomole ya taba fadar cewa, duk wanda ya shiga APC za a yafe masa zunubin da ya aikata ba.” In ji shi.

Dangane da sha’anin tsaro kuma, Sule Lamido ya ce akwai babbar matsala wajen magance tsaro a kasar nan, domin an samu gazawar shugabanci wanda kuma babban illa ce ga al’umma masu tasowa. Yana mai yin kiran a kara matsa kaimi don magance tsaro a kasar nan, da samun shugabanci nagari da zai hada kan matasa masu tasowa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma'aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.