ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ba Komai Ba Ce Illa Barin Jikin PDP Da Ya Rube – Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido ya bayyana cewa jam’iyyar APC ba komai ba ce illa rabin jikin PDP da ya rube, saboda kashi 80 na ‘ya`yan APC duk tsofaffin ‘yan PDP ne.

Sule Lamido ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da gidan talabijin na Arise a kwanan nan game da fagen siyasar Nijeriya.

  • Nijeriya Ta Musanta Iƙirarin Binance Na Zargin Cin Hancin Dala Miliyan 150
  • Majalisar Dattawa Za Ta Kafa Dokar Kare Hakkin ‘Yan Aikatau A Nijeriya 

Da yake mayar da martini kan maganar da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje ya yi a makon da ya gabata na cewa babu gurbi a kujerar shugabancin Nijeriya a 2027, Lamido ya ce magana ce kawai ta ‘yan siyasa, domin tsarin mulki ya bayar da damar gudanar da zabe duk bayan shekaru 4.

ADVERTISEMENT

Lokacin da aka tambaye shi game da ziyarar gwamnonin arewa a Amurka kan batun tsaro, ya ce yana matukar girmama ofishinsu na gwamnoni, amma ko kadan bai dace su tafi har Amurka ba saboda tattauna matsalolin tsaron Nijeriya.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta zo kan karagar mulki ne ba tare da manufofi ba, amma lokacin da PDP ke kan karagar mulki akwai dimbin manufofin da suka tsara gudanarwa domin ci gaban Nijeriya. Don haka ba za a taba hada hada gwamnatin PDP da ta APC ba, domin akwai bambanci sosai.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Kazalika, Sule Lamido ya ce sun ga yadda majan APC ta kasance ga ‘yan Nijeriya, wanda shi ya sa bai amince da manufar yin majar jam’iyyu saboda karbar mulki ba kawai, “na fi kaunar majan da za ta zo da kaykkyawar manufar yi wa ‘yan Nijeriya aiki. A lokacin da APC ta kulla maja a 2014 da sauran jam’iyyu ba su da wata mafufa illa iyaka su amshi shugabanci, sannan lokacin da suka hau karagar mulki kuma, majan ba ta amfanar da ‘yan Nijeriya ba. Don haka dole ne idan har za a yi maja ya kasance an bayyana manufofin da ake son cimmawa ba don amsar mulki ba kadai.”

Tsohon gwamnan, ya jaddada cewa lallai jam’iyyar PDP za ta dawo cikin hayyacinta duk da irin rikicin shugabanci da ta tsinci kanta a ciki. Yana mai cewar jam’iyyar ta shiga rikici mai yawan gaske ne sakamakon yadda wasu ‘ya`yanta ke yi wa APC aiki don durkusar da ita.

Ya bayyana yadda wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke ficewa daga jam’iyyar da cewa hukuncin kotu ne ya haddasa lamarin, sannan kuma wasu na jin tsoron Hukumar Yaki da Karya Tattalin Arzikin Kasa da Badakalar Kudi (EFCC), inda hakan ke sa su komawa jam’iyyar APC domin su kubuta daga zunubansu, “kamar yadda tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa, Adam Oshiomole ya taba fadar cewa, duk wanda ya shiga APC za a yafe masa zunubin da ya aikata ba.” In ji shi.

Dangane da sha’anin tsaro kuma, Sule Lamido ya ce akwai babbar matsala wajen magance tsaro a kasar nan, domin an samu gazawar shugabanci wanda kuma babban illa ce ga al’umma masu tasowa. Yana mai yin kiran a kara matsa kaimi don magance tsaro a kasar nan, da samun shugabanci nagari da zai hada kan matasa masu tasowa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma'aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.