ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
Jihohi

Majalisar dattawa ta bayyana cewa majalisar tarayya za ta duba dukkan muhimman abubuwan da suka dace kafin ta ba da shawarar da amincewa da kowanne bukata na kirkirar sabbin jihohi a duk fadin kasar.

Majalisar dattawan ta jaddada cewa, duk da dai wasu ‘yan Nijeriya na nema a kirkiro karin sabbin jihohi, za a kula da batun tare da gudanar da cikakken nazari tare da batun son kai ko bukatu na kashin kai ba.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Mai magana da yawun majalisar dattawa kuma shugaban kwamitin harkokin kafafen yada labarai, Sanata Yemi Adaramodu, ya bayyana hakan a karshen mako yayin da yake magana da manema labarai a gidansa da ke Ilawe-Ekiti cikin Jihar Ekiti. Ya bayyana cewa an riga an karbi kudirin bukatun kirkirar sabbin jihohi har guda 61.

ADVERTISEMENT

Sanatan, wanda ke wakiltar Yankin mazabar Ekiti ta Kudu, ya tabbatar da cewa za a bi hanyoyin da suka dace kafin a gabatar da kowanne kudiri.

Ya ce, “Zuwa yanzu dai, majalisar dattawa ta karbi kusan kudirorin bukatun kirkirar sabbin jihohi har guda 61. A cikin tattaunawarmu a lokacin sauraren jin ra’ayoyin jama’a a dukkan fadin kasar nan, an dai gabatar da wadannan bukatu a hukumance. Kamar yadda muka bayyana, dukkansu za a duba su da kuma yin kyakkyawan Nazari a kansu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Mun amshe bukatun, sannan bayan hakan kwamitin yin nazari kan sake yi wa tsarin mulki garambawul wanda mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Jibrin Barau yake jagoranta zai tattance tare da shirya rahoto ga majalisar.

“Da zarar rahoton ya kammala, majalisar dattawa tare da hadin gwiwar majalisar wakilai za su gudanar da cikakken jin ra’ayin jama’a. Wannan zai ba da dama ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da masu goyon baya da masu adawa su gabatar da hujjojinsu. Bayan haka, majalisun guda biyu za su yanke shawara kan wadannan bukatun.

“Batun kirkirar sabbin jihohi abu ne mai matukar muhimmanci wanda ke bukatar duba batutuwan al’umma, yankuna, da samun alkaluman tarihi. A wasu lokuta, ko a cikin jihohin da suka nema, ba a samu cikakken yarda ba. Dukkan wadannan abubuwan dole ne a yi la’akari da su. Kafin wannan, majalisaun tarayya ba su da hurumin amincewa da kirkirar wata sabuwar jiha.

“Kamar yadda ake ciki a halin yanzu, babu jihar da aka ba da shawara a kirkira. Ba za mu iya tabbatar da rahotanni na karshe ba ko zartar da hukunci kan jin ra’ayin jama’a da aka hada ba har sai an kammala sauraron jin ra’ayin jama’a gaba daya zuwa lokacin da muka dawo,” in ji shi.

Ya jaddada cewa ‘yan majalisar za su ba da muhimmanci ga sha’anin kasa sama da ra’ayoyinsu a yayin yanke shawarar kan batun yin garambawu a kundin tsarin mulkin kasar nan.

“Majalisar tarayya dai wuri ne na yin dokoki da kuma kula da aikin tsarawa ko gyara kundin tsarin mulki. Muna kira ga ’yan’uwanmu ‘yan majalisa su yi amfani da wannan dama da za ta dace ga kowa da kowa.

“Muna maraba da shawarwari daga dukkan ‘yan Nijeriya da suka hada da dattawa da kwararru da shugabannin siyasa da sarakunan gargajiya da kungiyoyin matasa da kungiyoyin mata da kungiyoyin farar hula, har ma da ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasashen waje.

“Za a bude taron sauraron jin ra’ayoyin jama’a ga kowa, kuma kundin na karshe kan gyara tsarin mulkin kasar nan zai bayyana batutuwan da ‘yan Nijeriya suka yanke hukunci a kai, ba ra’ayin wata kungiya kadai ba.

“Manufarmu ita ce, tabbatar da duk wasu canje-canje da za a yi a kundin tsarin mulki su kasance mafi kyawu ga bukatar Nijeriya da kuma mutanenta,” in ji Adaramodu.

Jihohi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.