ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Firaministan kasar Sin mista Li Keqiang ya ce, tattalin arzikin kasarsa ya hade da na duniya cikin wani matsayi mai zurfi, kana bude kofarta ga duniya wata babbar manufa ce ta kasar.

Saboda haka, Sin za ta tsaya kan wannan muhimmiyar manufa, gami da kokarin inganta harkoki a wannan fanni.

  • Wani Dan Kasuwan Kasar Sin Ya Bullo Da Shirin Magance Matsalar Gurbataccen Ruwa Sha A Nahiyar Afirka

Mista Li ya fadi haka ne a jiya Talata, yayin da yake halartar taron manyan ‘yan kasuwan kasashe daban daban karkashin laimar dandalin tattauna tattalin arzikin duniya, wanda ya gudana ta kafar bidiyo.

ADVERTISEMENT

A cewar firaministan kasar Sin, manufar bude kofar kasar ta shafi kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan kasar Sin za ta ci gaba da kokarin kare tsarin ciniki da ya shafi bangarori daban daban, da kungiyar ciniki ta duniya WTO take jagoranta, da sa kaimi ga yin ciniki cikin ‘yanci da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

Firaminista Li ya kara da cewa, kasarsa za ta kara kokarin daidaita muhallin gudanar da harkokin kasuwanci, da daukar matakan kandagarkin annobar COVID-19 masu dacewa, da kyautata yanayin ayyukan samar da izinin shiga kasar, da gudanar da gwajin kwayoyin cutar COVID-19. Haka kuma za ta taimakawa mutanen da suke neman yin ciniki ko aiki a kasashen ketare, don inganta mu’ammalar jama’ar Sin da ta kasashen waje.

Ban da wannan kuma, babban jami’in ya nanata cewa, kasar Sin za ta kiyaye manyan manufofinta na yanzu, don tabbatar da cimma burinta na raya tattalin arziki zuwa wani matsayin da take bukata, a wannan shekarar da muke ciki. Ya ce, sabon zagayen yaduwar cutar COVID-19 a duniya gami da sauran abubuwan da ba a iya hasashensu ba, sun sa tattalin arzikin Sin fuskantar matsi.

Duk da haka, a cewar firaministan, matakan daidaita yanayin da gwamnatin kasar Sin ta dauka, musamman ma wadanda suka shafi ba da tallafi ga kamfanoni, da shawo kan hauhawar farashin kayayyaki, sun yi amfani, inda suka sanya tattalin arzikin kasar komawa yanayi na karuwa, sai dai kuma ana bukatar daukar karin matakai don tabbatar da dorewar yanayin. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

LABARAI MASU NASABA

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.