• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Za Ta Tsaya Kan Manufar Bude Kofarta Ga Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Firaministan kasar Sin mista Li Keqiang ya ce, tattalin arzikin kasarsa ya hade da na duniya cikin wani matsayi mai zurfi, kana bude kofarta ga duniya wata babbar manufa ce ta kasar.

Saboda haka, Sin za ta tsaya kan wannan muhimmiyar manufa, gami da kokarin inganta harkoki a wannan fanni.

  • Wani Dan Kasuwan Kasar Sin Ya Bullo Da Shirin Magance Matsalar Gurbataccen Ruwa Sha A Nahiyar Afirka

Mista Li ya fadi haka ne a jiya Talata, yayin da yake halartar taron manyan ‘yan kasuwan kasashe daban daban karkashin laimar dandalin tattauna tattalin arzikin duniya, wanda ya gudana ta kafar bidiyo.

A cewar firaministan kasar Sin, manufar bude kofar kasar ta shafi kasashe masu sukuni, da wadanda ke kan hanyar tasowa.

Sa’an nan kasar Sin za ta ci gaba da kokarin kare tsarin ciniki da ya shafi bangarori daban daban, da kungiyar ciniki ta duniya WTO take jagoranta, da sa kaimi ga yin ciniki cikin ‘yanci da adalci.

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Firaminista Li ya kara da cewa, kasarsa za ta kara kokarin daidaita muhallin gudanar da harkokin kasuwanci, da daukar matakan kandagarkin annobar COVID-19 masu dacewa, da kyautata yanayin ayyukan samar da izinin shiga kasar, da gudanar da gwajin kwayoyin cutar COVID-19. Haka kuma za ta taimakawa mutanen da suke neman yin ciniki ko aiki a kasashen ketare, don inganta mu’ammalar jama’ar Sin da ta kasashen waje.

Ban da wannan kuma, babban jami’in ya nanata cewa, kasar Sin za ta kiyaye manyan manufofinta na yanzu, don tabbatar da cimma burinta na raya tattalin arziki zuwa wani matsayin da take bukata, a wannan shekarar da muke ciki. Ya ce, sabon zagayen yaduwar cutar COVID-19 a duniya gami da sauran abubuwan da ba a iya hasashensu ba, sun sa tattalin arzikin Sin fuskantar matsi.

Duk da haka, a cewar firaministan, matakan daidaita yanayin da gwamnatin kasar Sin ta dauka, musamman ma wadanda suka shafi ba da tallafi ga kamfanoni, da shawo kan hauhawar farashin kayayyaki, sun yi amfani, inda suka sanya tattalin arzikin kasar komawa yanayi na karuwa, sai dai kuma ana bukatar daukar karin matakai don tabbatar da dorewar yanayin. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

Matsalar Tsaro: Gwamnati Da Hukumomin Tsaro Sun Gaza – Masari

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.