• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Majar Jam’iyyun Adawa Na Iya Kawo Karshen Mulkin APC A 2027?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron da dan takarar shugaban kasa na jami’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na LP, Peter Obi ya sanya ana ta rade-raden cewa sun tattauna ne a kan yadda za su yi maja domin kwace mulki a hannun APC a 2027.

Atiku ya ce lallai wannan majar da za su yi abu ne mai yiwuwa a bisa dukkan alamu kuma suna da tabbacin cewa za a kai ga nasara don a cimma manufa.

  • PAN Ta Karrama Matar Gwamnan Jihar Zamfara Kan Kula Da Mata Da Marayu 
  • Firaministan Sin Ya Sauka A Seoul Domin Halartar Taron Kasashen Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu

Idan za a iya tunawa bayan ganawarsa da Peter Obi, Atiku ya bayar da tabbacin cewa ba damuwarsa ba ne ya janye wa wani don a sami nasara.
Haka kuma Peter Obi ya gana da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido.

Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar LP, Tanko Yunusa ya fitar da sanarwa bayan ganawar da ke cewa ziyarar na Peter Obi sun tattauna ne kan halin da kasa ke ciki.
Wani mai sharhin al’amuran yau da kullum, Julius Adegunna a bangarensa yana mai cewa wannan yunkuri abu ne mai kyau, wanda yake da shakku a cikinsa.

A cewarsa, mafi yawan ‘yan siyasan Nijeriya sun faye son ransu da kuma kwadayin mulki. Adegunna ya ce da zarar zabe ya gabato ne za a iya gane masu yi da gaske da masu neman abun duniya.
“‘Yan siyasar Nijeriya ba abun aminta ba ne. Sai dai kawai sadaukarwa ga wani fitaccen dan takara, idan ba haka ba kuma jam’iyyun adawa babu inda za su je.”

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A nasa gudunmuwar, wani mai sharhi a kan al’amuran da suka shafi kasa, Bishop Hebert Eke¬chukwu ya dauki lamarin ne ya kai can baya abun da ke faruwa a tarihi na yin maja a tsakanin jam’iyyun siyasar Nijeriya tun lokacin samaun ‘yancin kai a 1960.

“Jam’iyyar siyasa takan bayyana manufofinta da kudurorinta da duk wasu abubuwa da zai kai ta ga samun nasarar a zabe.

“A tsakanin shekaru 1962 zuwa 1966, wasu jam’iyyu sun rabu sakamakon rikicin cikin gida da aka samu a jam’iyyar AG da NCNC da NPC suka zama jam’iyya guda daya mai suna UPP karkashin jagorancin Cif S.L. Akintola

“A shekarar 1983, jam’iyyun UPN da NPP da wasu sun hada kai suka yi maja don kwatar mulki a hannun NPN, amma shirin bai samu nasara ba.

“Maja da za a ce shi ne mafi nasara a shekarar 2013, a lokacin da jam’iyyun ANPP da ACN da CPC da wasu bangare na APGA a Jihar Imo suka zama jam’iyyar APC, wannan dai shi ne lokaci na farko da aka kayar da gwamnatin PDP.

“Amma a daidai lokacin da ake fuskantar zaben 2027, ina ganin adawa mara karfi. ‘Yan siyasar da ake da su a yanzu sun faye kwadayi da son rai da nuna kabilanci.

“Ina da shakku matuka ko za a iya samun nasara a wannan majar. Amma a batun maja ana bukatar hada karfi da karfe kamar yadda Cif Olesugun Obasanjo ya yi a wancan lokaci.”

Haka kuma a wancan lokaci ba wai kawai jam’iyyun adawa ba ne suka yi maja har da wasu gwamnoni da sanatoci da ‘yan majalisun wakilai na PDP suka fice a jam’iyyar suka shiga cikin majar.

Rarrabuwar kai ta yadda kowa yake ganin idan ya tsaya a karin kansa zai iya kai wa ga nasara, hakan ta sanya Atiku da Peter Obi da Kwankwaso kowa ya ja tunga a zaben 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Jami’an Gwamnatin Kasa Da Kasa Suna Goyon-Bayan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Next Post

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 days ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

3 days ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

3 days ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

1 week ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

1 week ago
Next Post
Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

LABARAI MASU NASABA

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.