ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Majar Jam’iyyun Adawa Na Iya Kawo Karshen Mulkin APC A 2027?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Taron da dan takarar shugaban kasa na jami’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na LP, Peter Obi ya sanya ana ta rade-raden cewa sun tattauna ne a kan yadda za su yi maja domin kwace mulki a hannun APC a 2027.

Atiku ya ce lallai wannan majar da za su yi abu ne mai yiwuwa a bisa dukkan alamu kuma suna da tabbacin cewa za a kai ga nasara don a cimma manufa.

  • PAN Ta Karrama Matar Gwamnan Jihar Zamfara Kan Kula Da Mata Da Marayu 
  • Firaministan Sin Ya Sauka A Seoul Domin Halartar Taron Kasashen Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu

Idan za a iya tunawa bayan ganawarsa da Peter Obi, Atiku ya bayar da tabbacin cewa ba damuwarsa ba ne ya janye wa wani don a sami nasara.
Haka kuma Peter Obi ya gana da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar LP, Tanko Yunusa ya fitar da sanarwa bayan ganawar da ke cewa ziyarar na Peter Obi sun tattauna ne kan halin da kasa ke ciki.
Wani mai sharhin al’amuran yau da kullum, Julius Adegunna a bangarensa yana mai cewa wannan yunkuri abu ne mai kyau, wanda yake da shakku a cikinsa.

A cewarsa, mafi yawan ‘yan siyasan Nijeriya sun faye son ransu da kuma kwadayin mulki. Adegunna ya ce da zarar zabe ya gabato ne za a iya gane masu yi da gaske da masu neman abun duniya.
“‘Yan siyasar Nijeriya ba abun aminta ba ne. Sai dai kawai sadaukarwa ga wani fitaccen dan takara, idan ba haka ba kuma jam’iyyun adawa babu inda za su je.”

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

A nasa gudunmuwar, wani mai sharhi a kan al’amuran da suka shafi kasa, Bishop Hebert Eke¬chukwu ya dauki lamarin ne ya kai can baya abun da ke faruwa a tarihi na yin maja a tsakanin jam’iyyun siyasar Nijeriya tun lokacin samaun ‘yancin kai a 1960.

“Jam’iyyar siyasa takan bayyana manufofinta da kudurorinta da duk wasu abubuwa da zai kai ta ga samun nasarar a zabe.

“A tsakanin shekaru 1962 zuwa 1966, wasu jam’iyyu sun rabu sakamakon rikicin cikin gida da aka samu a jam’iyyar AG da NCNC da NPC suka zama jam’iyya guda daya mai suna UPP karkashin jagorancin Cif S.L. Akintola

“A shekarar 1983, jam’iyyun UPN da NPP da wasu sun hada kai suka yi maja don kwatar mulki a hannun NPN, amma shirin bai samu nasara ba.

“Maja da za a ce shi ne mafi nasara a shekarar 2013, a lokacin da jam’iyyun ANPP da ACN da CPC da wasu bangare na APGA a Jihar Imo suka zama jam’iyyar APC, wannan dai shi ne lokaci na farko da aka kayar da gwamnatin PDP.

“Amma a daidai lokacin da ake fuskantar zaben 2027, ina ganin adawa mara karfi. ‘Yan siyasar da ake da su a yanzu sun faye kwadayi da son rai da nuna kabilanci.

“Ina da shakku matuka ko za a iya samun nasara a wannan majar. Amma a batun maja ana bukatar hada karfi da karfe kamar yadda Cif Olesugun Obasanjo ya yi a wancan lokaci.”

Haka kuma a wancan lokaci ba wai kawai jam’iyyun adawa ba ne suka yi maja har da wasu gwamnoni da sanatoci da ‘yan majalisun wakilai na PDP suka fice a jam’iyyar suka shiga cikin majar.

Rarrabuwar kai ta yadda kowa yake ganin idan ya tsaya a karin kansa zai iya kai wa ga nasara, hakan ta sanya Atiku da Peter Obi da Kwankwaso kowa ya ja tunga a zaben 2023.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.