ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Majar Jam’iyyun Adawa Na Iya Kawo Karshen Mulkin APC A 2027?

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
APC

Taron da dan takarar shugaban kasa na jami’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar da takwaransa na LP, Peter Obi ya sanya ana ta rade-raden cewa sun tattauna ne a kan yadda za su yi maja domin kwace mulki a hannun APC a 2027.

Atiku ya ce lallai wannan majar da za su yi abu ne mai yiwuwa a bisa dukkan alamu kuma suna da tabbacin cewa za a kai ga nasara don a cimma manufa.

  • PAN Ta Karrama Matar Gwamnan Jihar Zamfara Kan Kula Da Mata Da Marayu 
  • Firaministan Sin Ya Sauka A Seoul Domin Halartar Taron Kasashen Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu

Idan za a iya tunawa bayan ganawarsa da Peter Obi, Atiku ya bayar da tabbacin cewa ba damuwarsa ba ne ya janye wa wani don a sami nasara.
Haka kuma Peter Obi ya gana da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido.

ADVERTISEMENT

Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar LP, Tanko Yunusa ya fitar da sanarwa bayan ganawar da ke cewa ziyarar na Peter Obi sun tattauna ne kan halin da kasa ke ciki.
Wani mai sharhin al’amuran yau da kullum, Julius Adegunna a bangarensa yana mai cewa wannan yunkuri abu ne mai kyau, wanda yake da shakku a cikinsa.

A cewarsa, mafi yawan ‘yan siyasan Nijeriya sun faye son ransu da kuma kwadayin mulki. Adegunna ya ce da zarar zabe ya gabato ne za a iya gane masu yi da gaske da masu neman abun duniya.
“‘Yan siyasar Nijeriya ba abun aminta ba ne. Sai dai kawai sadaukarwa ga wani fitaccen dan takara, idan ba haka ba kuma jam’iyyun adawa babu inda za su je.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

A nasa gudunmuwar, wani mai sharhi a kan al’amuran da suka shafi kasa, Bishop Hebert Eke¬chukwu ya dauki lamarin ne ya kai can baya abun da ke faruwa a tarihi na yin maja a tsakanin jam’iyyun siyasar Nijeriya tun lokacin samaun ‘yancin kai a 1960.

“Jam’iyyar siyasa takan bayyana manufofinta da kudurorinta da duk wasu abubuwa da zai kai ta ga samun nasarar a zabe.

“A tsakanin shekaru 1962 zuwa 1966, wasu jam’iyyu sun rabu sakamakon rikicin cikin gida da aka samu a jam’iyyar AG da NCNC da NPC suka zama jam’iyya guda daya mai suna UPP karkashin jagorancin Cif S.L. Akintola

“A shekarar 1983, jam’iyyun UPN da NPP da wasu sun hada kai suka yi maja don kwatar mulki a hannun NPN, amma shirin bai samu nasara ba.

“Maja da za a ce shi ne mafi nasara a shekarar 2013, a lokacin da jam’iyyun ANPP da ACN da CPC da wasu bangare na APGA a Jihar Imo suka zama jam’iyyar APC, wannan dai shi ne lokaci na farko da aka kayar da gwamnatin PDP.

“Amma a daidai lokacin da ake fuskantar zaben 2027, ina ganin adawa mara karfi. ‘Yan siyasar da ake da su a yanzu sun faye kwadayi da son rai da nuna kabilanci.

“Ina da shakku matuka ko za a iya samun nasara a wannan majar. Amma a batun maja ana bukatar hada karfi da karfe kamar yadda Cif Olesugun Obasanjo ya yi a wancan lokaci.”

Haka kuma a wancan lokaci ba wai kawai jam’iyyun adawa ba ne suka yi maja har da wasu gwamnoni da sanatoci da ‘yan majalisun wakilai na PDP suka fice a jam’iyyar suka shiga cikin majar.

Rarrabuwar kai ta yadda kowa yake ganin idan ya tsaya a karin kansa zai iya kai wa ga nasara, hakan ta sanya Atiku da Peter Obi da Kwankwaso kowa ya ja tunga a zaben 2023.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

Rikicin ADC: Ibrahim Little Ya Ƙaryata Zargin Ƙaƙabawa Jam’iyyar Shugabanni

June 21, 2026
Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

Mutumin Da Ya Yi Matukar Tasiri Kan Shugaba Xi Jinping

June 21, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

Ƴansanda Sun Kama Mutane 5 Kan Satar Wayoyin Lantarki A Katsina

June 21, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.