• English
  • Business News
Sunday, June 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Sun Mayar Da Martani Game Da Cika Shekara Daya Na Mulkin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
jam'iyyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan adawa sun siffanta mulkin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na tsawon shekara daya a matsayin bai tsinana wa ‘yan Nijeriya da komi ba.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya bayyana cewa shekarar farko na mulkin Tinubu bai haifar da da mai ido ba, saboda bai aiwatar da wani tsari na a zo a gani ba.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitara a ranar Talata.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

A cewarsa, lokacin da aka rantsar da Tinubu ya lasa wa ‘yan Nijeriya zuma a baki na cewa zai farfado da tattalin arziki da samar da ayyukan yi da samar da tsaro da kawo karshen fatara a kasar nan.

Atiku ya ce lokacin da ‘yan Nijeriya suka ji kalamansa sai suka dauka zai kawo musu sauki a kan ukubar da suka sha na mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na tsawon shekara 8.

“Tinubu bai yi wani tsari kan sake farfado da tattalin arziki ba, sai dai ma ya kara dagula lamura.
“A watan Mayun 2023, ya cire tallafin man fetur, bayan wata daya kuma, babban bankin Nijeriya ya kaddamar da sabon tsari kan hada-hadar canjin kudaden waje na bai daya.

Labarai Masu Nasaba

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

“Wadannan tsari sun yi matukar raunata tattalin arzikin kasar nan, wanda suka kara talauta ‘yan Nijeriya tun daga wannan lokaci har zuwa yau.”

A nasa bangaren, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya siffanta shekara daya na mulkin Tinubu a matsayin gazawa ta karshe.

Sowore idan shi malami ne zai rushe ajin da Tinubu yake da ya ba shi maki. Dan takarar shugaban kasan na AAC ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita.

“Idan ni malami ne ba zan taba bai wa Tinubu maki kan mulkinsa na shekara guda ba, ni zan ma rutse ajin ne saboda babu abin da za a iya ba shi na maki.

“Ina mai tabbatar da cewa wannan mulki na shekara guda ba mu karu da komi ba. An samu hauhawar farashin kayayyaki wanda ba a taba samu ba, rashin ayyukan yi ya kara kazanta, rashin tsaro ya kara ta’azzara a cikin shekara daya, sannan kuma gwamnati ta kasa biyan mafi karancin albashi.”

Su kuwa ‘yan majalisa na jam’iyyar LP sun bayyana cewa Tinubu bai cika alkawarin da ya yi wa ‘yan Nijeriya lokacin yakin neman zabe a tsawon mulkinsa na shekara daya ba.

Sun ce an samu karuwar rashin tsaro da matsin tattailin arziki a tsawon mulkin Tinubu na shekara guda.
‘Yan majalisar karkashin jagorancin Afam Ogene ya ce ‘yan Nijeriya za a tambaya ko Tinubu ya cika alkawarin da ya yi a cikin shekara guda.

Sun dai yi Kiara da Shugaba Tinubu da ya gaggauta rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke fama da shi a halin yanzu, tare da tabbatar an samu wadataccen abinci da ruwan sha da kiwon lafiya da kuma ingantaccen ilimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCJam'iyyun SiyasaNNPPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Nijeriya Ga ‘Yan Majalisa: Yunwa Ta Fi Damun Mu Ba Sauya Taken Kasa Ba

Next Post

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

Related

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano
Labarai

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

3 hours ago
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027
Manyan Labarai

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

5 hours ago
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
Labarai

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

9 hours ago
Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda
Labarai

Babban Hafsan Soji Ya Ƙalubalanci Sabbin Sojoji Da Su Shirya Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda

9 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa
Manyan Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Tsawa Da Ruwan Sama Na Tsawon Kwanaki A Arewa

11 hours ago
An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
Labarai

An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 

15 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

LABARAI MASU NASABA

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

Wata Sabuwa: Malaman Jami’ar Tarayya A Kano Sun ƙi Amince Wa Da Zaɓen Sabon VC

June 15, 2025
PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin

June 15, 2025
An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa Karo Na 27 Na Shanghai

June 15, 2025
Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

Yansanda Sun Fara Tsananta Daukar Mataki Kan Yan Daba A Kano

June 15, 2025
Dan Asalin Tudun Loess

Dan Asalin Tudun Loess

June 15, 2025
Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

Ba Zai Manta Da Shawarar Mahaifinsa Ba

June 15, 2025
Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027

June 15, 2025
Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila

June 15, 2025
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

June 15, 2025
NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka

June 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.