• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

’Yan Adawa Sun Mayar Da Martani Game Da Cika Shekara Daya Na Mulkin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
jam'iyyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan adawa sun siffanta mulkin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu na tsawon shekara daya a matsayin bai tsinana wa ‘yan Nijeriya da komi ba.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar ya bayyana cewa shekarar farko na mulkin Tinubu bai haifar da da mai ido ba, saboda bai aiwatar da wani tsari na a zo a gani ba.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitara a ranar Talata.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  • Sojojin Nijar Sun Cafke Kasurgumin Dan Bindigar Da Ya Addabi Zamfara

A cewarsa, lokacin da aka rantsar da Tinubu ya lasa wa ‘yan Nijeriya zuma a baki na cewa zai farfado da tattalin arziki da samar da ayyukan yi da samar da tsaro da kawo karshen fatara a kasar nan.

Atiku ya ce lokacin da ‘yan Nijeriya suka ji kalamansa sai suka dauka zai kawo musu sauki a kan ukubar da suka sha na mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari na tsawon shekara 8.

“Tinubu bai yi wani tsari kan sake farfado da tattalin arziki ba, sai dai ma ya kara dagula lamura.
“A watan Mayun 2023, ya cire tallafin man fetur, bayan wata daya kuma, babban bankin Nijeriya ya kaddamar da sabon tsari kan hada-hadar canjin kudaden waje na bai daya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

“Wadannan tsari sun yi matukar raunata tattalin arzikin kasar nan, wanda suka kara talauta ‘yan Nijeriya tun daga wannan lokaci har zuwa yau.”

A nasa bangaren, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore, ya siffanta shekara daya na mulkin Tinubu a matsayin gazawa ta karshe.

Sowore idan shi malami ne zai rushe ajin da Tinubu yake da ya ba shi maki. Dan takarar shugaban kasan na AAC ya bayyana hakan ne a shafinsa na Tuwita.

“Idan ni malami ne ba zan taba bai wa Tinubu maki kan mulkinsa na shekara guda ba, ni zan ma rutse ajin ne saboda babu abin da za a iya ba shi na maki.

“Ina mai tabbatar da cewa wannan mulki na shekara guda ba mu karu da komi ba. An samu hauhawar farashin kayayyaki wanda ba a taba samu ba, rashin ayyukan yi ya kara kazanta, rashin tsaro ya kara ta’azzara a cikin shekara daya, sannan kuma gwamnati ta kasa biyan mafi karancin albashi.”

Su kuwa ‘yan majalisa na jam’iyyar LP sun bayyana cewa Tinubu bai cika alkawarin da ya yi wa ‘yan Nijeriya lokacin yakin neman zabe a tsawon mulkinsa na shekara daya ba.

Sun ce an samu karuwar rashin tsaro da matsin tattailin arziki a tsawon mulkin Tinubu na shekara guda.
‘Yan majalisar karkashin jagorancin Afam Ogene ya ce ‘yan Nijeriya za a tambaya ko Tinubu ya cika alkawarin da ya yi a cikin shekara guda.

Sun dai yi Kiara da Shugaba Tinubu da ya gaggauta rage wa ‘yan Nijeriya wahalhalun da suke fama da shi a halin yanzu, tare da tabbatar an samu wadataccen abinci da ruwan sha da kiwon lafiya da kuma ingantaccen ilimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCJam'iyyun SiyasaNNPPPDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

’Yan Nijeriya Ga ‘Yan Majalisa: Yunwa Ta Fi Damun Mu Ba Sauya Taken Kasa Ba

Next Post

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

Related

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 
Manyan Labarai

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

2 hours ago
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

6 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

7 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

8 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

9 hours ago
Next Post
Manzon Allah

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (4): Manzon Allah (SAW) Bai Taba Barin Azumtar Kwanakin Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.