• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Tana Fatan Bayar Da Gudummawa Ga Inganta Mu’ammalar Wayewar Kai Da Ci Gaban Duniya

by CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Tana Fatan Bayar Da Gudummawa Ga Inganta Mu’ammalar Wayewar Kai Da Ci Gaban Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian, ya ce kudurin da aka zartas a babban taron MDD kwanan nan, mai nasaba da samar da “Ranar tattauna harkokin wayewar kai ta duniya” wanda Sin ta gabatar, ya nuna cewa ajandar raya wayewar kan duniya ta dace da bukatun zamani, kuma ra’ayoyi, da dabarun Sin suna samun karbuwa, da goyon baya, da amsa daga kasashe da dama. 

Lin Jian wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, yayin da ya jagoranci taron manema labarai na rana rana da aka saba gudanarwa, ya ce Sin tana fatan yin aiki tare da al’ummun duniya, don karfafa mu’amala tsakanin wayewar kan al’ummmin kasa da kasa, da kuma inganta zaman lafiya da ci gaban duniya.

  • Mataimakin Shugaban Kasar Malawi Ya Rasu Hatsarin Jirgin Sama
  • Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika

Game da kare kayan tarihi na duniya kuwa, Lin Jian ya ce, Sin tana da abubuwan tarihi 57, wadanda aka saka a jerin kayan tarihi na duniya, kuma wannan adadi ya zama na biyu a duniya. Kaza lika Sin tana son sanya hikima, da karfinta don habaka ci gaban kayan tarihi na duniya ba tare da kasala ba.

Game da binciken gano ko motoci masu aiki da lantarki kirar kasar Sin sun samu tallafi daga gwamnatin Sin din ko a’a, wanda EU ta kuduri aniyar gudanarwa kuwa, Lin Jian ya ce, Sin na kira ga EU da ta gaggauta dakatar da binciken, don gujewa gurgunta dangantakar kasuwanci, da zaman lafiya a tsarin samar da kayayyaki, da ayyukan masana’antu tsakanin Sin da EU.

Don gane da zargin da Amurka ta yayata cewa wai “Sin na haifar da barazanar makaman nukiliya”, Lin Jian ya ce, Sin na shawartar Amurka da ta ci gaba da rage yawan makaman nukiliyarta bisa gaskiya, maimakon jefa zargin hakan ga sauran kasashe.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Sai kuma batun taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar BRICS, wanda aka gudanar kwanan nan, inda Lin Jian ya ce, ya kamata a daga matsayin kungiyar BRICS zuwa wani sabon tsarin hadin gwiwa na bangarori daban-daban, bisa sabbin kasuwanni da kasashe masu tasowa, wanda ke bude wa kowa kofa, tare da kasancewa damar cudanyar kasa da kasa.

Game da “Ra’ayoyi shida” na Sin da Brazil, don gane da warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa, wadanda suka samu karbuwa tsakanin kasashe da dama na duniya kuwa, Lin Jian ya ce, Sin tana maraba da karin kasashe masu goyon baya, da kuma rungumar “Ra’ayoyin shida”. (Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DuniyaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwalara Ta Kashe Mutane 5 A Lagos, An Kai 60 Asibiti Ranga-Ranga

Next Post

Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

2 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

3 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

5 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

8 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

9 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

10 hours ago
Next Post
Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

Jirgin Ƙasan Kaduna Zuwa Kano Zai Fara Aiki Farkon 2025 

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.