ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika

by Abubakar Sulaiman
2 years ago
Hadi Sirika

Alleged N2.8bn Fraud: EFCC Opens Case Against Sirika, Others

Zargin Almundahanar Biliyan ₦2.8b: EFCC Ta Gurfanar Da Hadi Sirika Gaban Kotu

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa, EFCC, ta fara tuhumar tsohon ministan sufurin jiragen sama, Hadi Sirika da wasu mutane uku, bisa zargin almundahanar Naira biliyan 2.6.

ADVERTISEMENT

Sirika, tare da ɗiyar sa Fatima, Jalal Sule Hamma, da kuma Al-Duraq Investment Limited, suna fuskantar tuhume-tuhume guda shida da suka haɗa da zamba a ofis da kuma badaƙalar kwangila a babbar kotun birnin tarayya (FCT) dake Maitama.

  • Badakalar Fiye Da Biliyan 8: EFCC Ta Cafke Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika 
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Shaidu na farko na EFCC, Azubuike Okorie, tsohon ma’aikacin ma’aikatar sufurin jiragen sama, ya shaida rawar da ya taka a matsayinsa na Daraktan saye da sayarwa da kuma mataimaki na musamman ga Ministan, inda ya bayyana ayyukan sa na sa ido da tantance ayyuka, duk da cewa ba shi da hannu kai tsaye wajen bayar da kwangila.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Okorie ya bayyana cewa kwamitin aiwatar da ayyukan da ya jagoranta ya gano rashin jituwa a lokacin da ake sa ido kan ayyukan musamman a filin jirgin saman Katsina, inda babu wani ɗan kwangila da yake gudanar da aiki ciki har da Al-Duraq, duk da cewa akwai sunayensu matsayin ƴan kwangila.

Ya shaida cewar har ya kammala aikin gwamnati a watan Mayun 2023, ba a aiwatar da aikin kwangilar da kamfanin Al-Duraq ba wacce ta kai Naira miliyan 800. Ya ƙara da cewa, yana da masaniyar wani kuɗi da aka biya wa Al-Duraq kashi 30 cikin 100 na tara kuɗaɗen shiga, amma babu hannun shi cikin tsarin biyan kuɗi wanda aka yi shi bisa ƙa’ida ba.

Kanu Agabi, SAN, Lauyan Sirika, ya buƙaci da a ɗage zaman domin duba takardun ƙarar, buƙatar da wasu lauyoyin masu ƙara suka goyi bayan kuma masu gabatar da ƙara ba su yi hamayya ba.

Sakamakon haka, Mai shari’a Sylvanus Oriji ya ɗage sauraron ƙarar har zuwa ranar 30 ga wata domin yi masa tambayoyi da kuma ci gaba da shari’ar.

Hadi Sirika
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Sin: Ana Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Hadin Gwiwa A Nahiyar Asiya

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.