• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kara Mu’amala Tsakanin Mabambantan Al’ummomin Duniya Zai Kawar Da Sabani Da Rashin Fahimta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duniyar yanzu, babbar matsalar dake haifar da tashe-tashen hankula da rashin girmama juna ita ce, rashin fahimta da mu’amala tsakanin mabambantan al’ummomi. Matukar ana son yi wa tufkar hanci tare da samun duniya mai fahimta da zaman lafiya, sai an inganta mu’amala tsakanin mabambantan al’ummomin duniya.

A karshen makon da ya gabata ne, yayin zaman babban zauren MDD na 78, daukacin mambobin majalisar suka amince da kudurin da Sin ta gabatar na ware wata rana, domin inganta mu’amala da tattaunawa tsakanin mabambantan al’ummomin duniya, inda aka ayyana ranar 10 ga watan Yunin kowacce shekara ta kasance wannan rana.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

Hakika hangen nesa irin na kasar Sin ya cancanci yabo. Har kullum cikin bangarorin da take mayar da hankali kansu a hadin gwiwarta da kasa da kasa shi ne, inganta mu’amala da musaya tsakanin al’ummomi, da zummar kyautata fahimta da koyi da juna. Misali, a baya-bayan nan, an yi taron musaya tsakanin matasan Sin da Afrika a birnin Beijing, kuma wannan wani taro ne da kasar Sin kan dauki nauyinsa a kowacce shekara. Ba wannan kadai ba, a ko da yaushe kasar Sin na samar da tallafin karatu ga matasan kasashen duniya daban-daban, domin su zo kasar su yi karatu da mu’amala da takwarorinsu da kuma kara fahimtar al’adu da yanayin kasar, da zummar kawar da sabani da bahaguwar fahimta. Idan zan bada misali da kai na, tabbas ra’ayi da tunanina game da kasar Sin sun sauya bayan zuwana kasar tare da mu’amala da jama’arta, ke nan, lallai mu’amala da cudanya na kara wayar da kan jama’a da samar da fahimtar juna.

Har ila yau a gainina, bambancin al’ada ko addini ko launin fata dake akwai tsakanin al’ummomin duniya, abun alfahari ne ga dan adam, sannan wata dama ce ta karin ilimi. Kowacce al’ada ko kabila na da nata sigogi na musamman, kuma ta hanyar mu’amala da musaya ne kadai, mabambantan al’ummomi za su iya fahimta da hakuri da girmama juna da kuma samun jituwa. Lamarin da zai kai ga samun zaman lafiya da girmama juna, wanda shi ne burin kasar Sin a ko da yaushe.

Dukkan bil adama matsayi daya gare su, babu wanda ya fi wani. Gane darajar dan adam da hakuri da girmama juna ba zai samu ba, har sai an fahimci juna an kuma ma’amalantu. Fatan ita ce, wannan rana da aka ayyana ta taka rawar gani wajen kawo zaman lafiya da dunkulewar al’ummun duniya cikin kwanciyar hankali da lumana. (Faeza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban duniyaDuniya labariKoriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Dimokuraɗiyyar:  Ƴan Nijeriya Fushi Suke, PDP Ga Tinubu 

Next Post

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

15 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

16 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

17 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

18 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

19 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

20 hours ago
Next Post
Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

Rusau: ‘Yan Kasuwar Kano 5,000 Za Su Rasa Shagunansu Bayan Shafe Shekaru 18 A Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.