• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce aikin shimfiɗa bututun gas daga Ajaokuta-Kaduna-Kano (AKK) zai bunƙasa hanyoyin tattalin arzikin Arewacin Nijeriya.

A takardar sanarwa ga manema labarai da ya rattaba wa hannu, mai ba ministan shawara kan aikin jarida, Malam Rabiu Ibrahim, ya ce, Idris ya bayyana haka ne a Kaduna a lokacin da ya kai ziyara wurin aikin bututun gas na AKK da ake yi a gaɓar Kogin Kaduna.

  • Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto
  • Manoman Kano Da Kaduna Za Su Amfana Da Shirin Yaki Da Cutar Tumatir

Ya halarci wurin ne tare da rakiyar Ministan Kuɗi, Wale Edun; da Ƙaramin Ministan Albarkatun Gas, Mista Ekperikpe Ekpo, da kuma Shugaban Kamfanin NNPC, Mele Kyari.

A jawabinsa a wajen ziyarar, Idris ya ce, “Aikin na AKK ya mayar da hankali ne wajen fitar da ɗimbin ƙarfin tattalin arzikin Arewacin Nijeriya. Gas ɗin da za a yi jigilarsa zai samar da makamashin da ake buƙata ga gidaje, kasuwanci, da masana’antu, sannan kuma zai ba da damar hada-hadar sufuri da rage farashin sa.

“Ci gaba da aiwatar da wannan aiki, wanda shi ne babban aikin bututun gas na cikin gida a Nijeriya zuwa yanzu, wanda gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta yi, wata alama ce da ke nuni da ƙudirin Shugaban Ƙasa na bunƙasa masana’antu da ci gaban tattalin arzikin kowane ɓangare na ƙasar nan.”

Labarai Masu Nasaba

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

Haka kuma ya yaba da aikin a matsayin mai muhimmanci ga cigaban masana’antu da tattalin arzikin Nijeriya a ƙarƙashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana shi a matsayin aikin bututun gas na cikin gida mafi girma a ƙasar.

Ministan ya kuma danganta cigaban tattalin arziki da tsaro, inda ya ce yawancin matsalolin tsaro da ake fama da su a Arewacin Nijeriya suna faruwa ne sakamakon taɓarɓarewar tattalin arziki, wanda za a iya ragewa ta hanyar samar da ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziƙi.

Ya ce, “Samar da makamashi a gidaje, gonaki, da masana’antu ya na da matuƙar muhimmanci ga samar da ayyukan yi masu yawa.”

Idris ya bayyana yiwuwar aikin zai taimaka wa harkar noma sosai a Arewacin Nijeriya.

Bugu da ƙari, ya yi nuni da irin tasirin da irin waɗannan ayyuka ke yi a faɗin ƙasar nan, inda ya ce a watan da ya gabata an ƙaddamar da wasu muhimman ayyukan samar da gas guda uku a yankin Neja Delta.

Ya ƙara da cewa aikin na AKK zai tallafa wa Shirin Shugaban Ƙasa na Gas (Pi-CNG), wanda tuni ya jawo jarin sama da dalar Amurka miliyan 50.

Ya ce, “Aikin bututun na AKK wani ginshiƙin fata ne, wanda zai farfaɗo da tattalin arzikin dukkan ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AkkCNGKRPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

Next Post

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

Related

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

2 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

3 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

4 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

16 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

18 hours ago
Next Post
Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Sin Ta Kalubalanci Kasashen Yammacin Duniya Da Su Tuna Da Laifinsu Na Mulkin Mallaka

Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba

June 30, 2025
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

June 30, 2025
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.