ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Yayin da musulmai suka yi bikin Babbar Sallah, hukumar kula da ilimin Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta, ta kara jaddada aniyarta ta daukar nauyin yara miliyan 10 da ba sa zuwa makaranta daga nan zuwa shekara ta 2027.

Babban Sakatare kuma Shugaban Hukumar; Dakta Muhammad Sani Idris, shi ne ya bayyana haka a sakonsa na barka da Sallah a ranar Lahadin da ta gabata, sannan ya jinjina wa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, na taimaka wa yara wadanda ba sa zuwa makaranta, inda ya kara jaddada mayar da hankali a kan lamarin ilimin yaran.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kamar yadda ya ce, hukumar na matukar yin kokari yadda ya kamata; wajen kula tare da koyar da almajirai ilimi, inda ya kara jaddada aniyar tasu ta samar da tsarin ilimi mai nagarta, wanda zai bai wa yaran da ba sa zuwa makaranta damar samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, “Ina isar da gaisuwata ga dukkanin al’ummar Nijeriya, wadanda suke yi mana fata na musamman; dangane da wannan daukar nauyi da wannan hukuma ke yi dangane abubuwan da suka shafi ilimin almajirai da yara kanana, wadanda ba sa zuwa makaranta.

“Ina yin kira ga masu ruwa da tsaki, da su kara mayar da hankali tare da himmatuwa a kan wannan lamari da ya shafi ilimi. Domin kuwa, ta hanyar ilimi ne kadai ake iya bai wa matasa dama, inda za su nuna kwazonsu domin a taimaka masu su kasance wadanda za su taimakawa al’umma a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

“Ina mai nuna farincikina, a kan irin niyyar da Tinubu yake da ita na kawar da matsalolin da almajirai da yara kanana wadanda ba sa zuwa makaranta ke fuskanta a Nijeriya. Kulawar da yake nunawa a kan lamarin ilimi da ci gaban al’umma, hakan yana kara nuna wa ‘yan Nijeriya yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali ga jin dadin ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda suke da bukatar a taimaka musu.

Bugu da kari ya ce, “Muna yin kokari wajen ganin sa lamarin ilimin Boko a cikin tsarin yadda za a koyar da wadannan almajira ,domin su ma su samu kyakkyawar rayuwa.

“Za kuma mu ci gaba da tuntuba da kuma yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki, wadanda suka hada da ma’aikatar ilimi ta tarayya da masu taimaka wa ci gaban ilimi, jihohi da kananan hukumomi, da su yi kokari wajen taimakawa dangane da matsalolin da suke addabar wadannan yara.

“Tsarin shugabanci na Shugaban Kasa Tinubu, na matukar taimakawa wajen cimma muradun; musamman ta yadda aka faro. Sannan, muna da tabbacin za mu tabbatar da sai kowane yaro ya kai ga samun hanyar samun ilimi mai nagarta ba tare da la’akari da yadda suka taso ko matsalolin da suke fuskanta ba”.

Almajirai
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

LABARAI MASU NASABA

Almajirai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Almajirai

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Almajirai

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Almajirai

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.