ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Yayin da musulmai suka yi bikin Babbar Sallah, hukumar kula da ilimin Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta, ta kara jaddada aniyarta ta daukar nauyin yara miliyan 10 da ba sa zuwa makaranta daga nan zuwa shekara ta 2027.

Babban Sakatare kuma Shugaban Hukumar; Dakta Muhammad Sani Idris, shi ne ya bayyana haka a sakonsa na barka da Sallah a ranar Lahadin da ta gabata, sannan ya jinjina wa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, na taimaka wa yara wadanda ba sa zuwa makaranta, inda ya kara jaddada mayar da hankali a kan lamarin ilimin yaran.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kamar yadda ya ce, hukumar na matukar yin kokari yadda ya kamata; wajen kula tare da koyar da almajirai ilimi, inda ya kara jaddada aniyar tasu ta samar da tsarin ilimi mai nagarta, wanda zai bai wa yaran da ba sa zuwa makaranta damar samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, “Ina isar da gaisuwata ga dukkanin al’ummar Nijeriya, wadanda suke yi mana fata na musamman; dangane da wannan daukar nauyi da wannan hukuma ke yi dangane abubuwan da suka shafi ilimin almajirai da yara kanana, wadanda ba sa zuwa makaranta.

“Ina yin kira ga masu ruwa da tsaki, da su kara mayar da hankali tare da himmatuwa a kan wannan lamari da ya shafi ilimi. Domin kuwa, ta hanyar ilimi ne kadai ake iya bai wa matasa dama, inda za su nuna kwazonsu domin a taimaka masu su kasance wadanda za su taimakawa al’umma a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

“Ina mai nuna farincikina, a kan irin niyyar da Tinubu yake da ita na kawar da matsalolin da almajirai da yara kanana wadanda ba sa zuwa makaranta ke fuskanta a Nijeriya. Kulawar da yake nunawa a kan lamarin ilimi da ci gaban al’umma, hakan yana kara nuna wa ‘yan Nijeriya yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali ga jin dadin ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda suke da bukatar a taimaka musu.

Bugu da kari ya ce, “Muna yin kokari wajen ganin sa lamarin ilimin Boko a cikin tsarin yadda za a koyar da wadannan almajira ,domin su ma su samu kyakkyawar rayuwa.

“Za kuma mu ci gaba da tuntuba da kuma yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki, wadanda suka hada da ma’aikatar ilimi ta tarayya da masu taimaka wa ci gaban ilimi, jihohi da kananan hukumomi, da su yi kokari wajen taimakawa dangane da matsalolin da suke addabar wadannan yara.

“Tsarin shugabanci na Shugaban Kasa Tinubu, na matukar taimakawa wajen cimma muradun; musamman ta yadda aka faro. Sannan, muna da tabbacin za mu tabbatar da sai kowane yaro ya kai ga samun hanyar samun ilimi mai nagarta ba tare da la’akari da yadda suka taso ko matsalolin da suke fuskanta ba”.

Almajirai
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Almajirai
Ilimi

An Tantance Masu Neman Aikin Koyarwa 500 A Jigawa

August 31, 2026
Almajirai
Ilimi

JAMB Ta Ƙara Wa’adin Amincewar Guraben Karatu Zuwa 30 Satumba

August 29, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Next Post
Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.