ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Kula Da Ilimin Almajirai Da Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Za Ta Saka Yara Miliyan 10 A Makarantu

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Almajirai

Yayin da musulmai suka yi bikin Babbar Sallah, hukumar kula da ilimin Almajirai da yaran da ba sa zuwa makaranta, ta kara jaddada aniyarta ta daukar nauyin yara miliyan 10 da ba sa zuwa makaranta daga nan zuwa shekara ta 2027.

Babban Sakatare kuma Shugaban Hukumar; Dakta Muhammad Sani Idris, shi ne ya bayyana haka a sakonsa na barka da Sallah a ranar Lahadin da ta gabata, sannan ya jinjina wa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, na taimaka wa yara wadanda ba sa zuwa makaranta, inda ya kara jaddada mayar da hankali a kan lamarin ilimin yaran.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kamar yadda ya ce, hukumar na matukar yin kokari yadda ya kamata; wajen kula tare da koyar da almajirai ilimi, inda ya kara jaddada aniyar tasu ta samar da tsarin ilimi mai nagarta, wanda zai bai wa yaran da ba sa zuwa makaranta damar samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, “Ina isar da gaisuwata ga dukkanin al’ummar Nijeriya, wadanda suke yi mana fata na musamman; dangane da wannan daukar nauyi da wannan hukuma ke yi dangane abubuwan da suka shafi ilimin almajirai da yara kanana, wadanda ba sa zuwa makaranta.

“Ina yin kira ga masu ruwa da tsaki, da su kara mayar da hankali tare da himmatuwa a kan wannan lamari da ya shafi ilimi. Domin kuwa, ta hanyar ilimi ne kadai ake iya bai wa matasa dama, inda za su nuna kwazonsu domin a taimaka masu su kasance wadanda za su taimakawa al’umma a nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

“Ina mai nuna farincikina, a kan irin niyyar da Tinubu yake da ita na kawar da matsalolin da almajirai da yara kanana wadanda ba sa zuwa makaranta ke fuskanta a Nijeriya. Kulawar da yake nunawa a kan lamarin ilimi da ci gaban al’umma, hakan yana kara nuna wa ‘yan Nijeriya yadda gwamnatinsa ta mayar da hankali ga jin dadin ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda suke da bukatar a taimaka musu.

Bugu da kari ya ce, “Muna yin kokari wajen ganin sa lamarin ilimin Boko a cikin tsarin yadda za a koyar da wadannan almajira ,domin su ma su samu kyakkyawar rayuwa.

“Za kuma mu ci gaba da tuntuba da kuma yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki, wadanda suka hada da ma’aikatar ilimi ta tarayya da masu taimaka wa ci gaban ilimi, jihohi da kananan hukumomi, da su yi kokari wajen taimakawa dangane da matsalolin da suke addabar wadannan yara.

“Tsarin shugabanci na Shugaban Kasa Tinubu, na matukar taimakawa wajen cimma muradun; musamman ta yadda aka faro. Sannan, muna da tabbacin za mu tabbatar da sai kowane yaro ya kai ga samun hanyar samun ilimi mai nagarta ba tare da la’akari da yadda suka taso ko matsalolin da suke fuskanta ba”.

Almajirai
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    ‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

MASU ALAKA

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

Sabulu Na Musamman Domin Gyaran Fata Da Hadin Dilka

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.