ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

Makarantu da dama a halin yanzu, ba su da kayan aikin da ya kamata a ce suna da su, musamman domin taimaka wa koyarwar ta kasance cikin sauki.

Haka nan, idan ana maganar darussan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha, makarantun da suke da wadannan kayan aiki har gara ma a ce ba su da su; sakamakon rashin ingancinsu.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kazali, dakunan karatu babu littattafan zamani da mukalu da kuma mujallun da za su taimaka wa harkokin koyo da koyarwar.

ADVERTISEMENT

Rashin tarbiyya na taimakawa wajen aikata magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, fyade da sauransu, wadanda ke taimakawa wajen gurgunta ci gaban ilimi.

Bincike ya gano cewa, akwai wasu cibiyoyin rubuta jarabawa; inda iyaye ke ba da kudi, domin ‘ya’yansu su samu sakamako mai kyau a jarrabawar kammala sakandare tare kuma da samun makin da ya dace, don samun cancantar shiga jami’a ko sauran makarantun da ke gaba da sakarandire.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Har ila yau, rashin kulawar iyaye shi ne babban abin da ya sa ake haduwa ko samun nakasu a bangaren ilimi. Domin kuwa, su ne garkuwa wajen kulawa da rayuwar ‘ya’yansu, musamman ta fuskar ba su tarbiyya da karatunsu da kuma sauran al’amuran rayuwarsu.

Akwai abubuwan da suke taimaka wa malamai wajen aikinsu na koyarwa, wadanda da ma da su ne suke amfani wajen jan hankalin dalibai; don mayar da hankalinsu kan abubuwan da ake koya masu.

Wadannan abubuwa sun hada da wadanda za su ji da na gani, littattafai, komfuta da sauransu, ba a samar wa malamai irin wadannan kayayyakin da za su taimaka musu wajen gudanar da aikinsu daga karshe, sai koyarwar ta zamar musu da wahala.

Babu wani tsarin ilimi da aka sama wa malamai, don yadda za su samar da ilimi mai nagarta ga dalibai, shi ya sa yawancin makarantu ba sa iya tafiya da tsari ko wani abu mi tasiri wanda zai yi kama da irin tsarin Kasar Ingila.

Ba kamar sauran sassa ko bangare ba, inda dalibai suke rubibin samun gurbinsu na makaranta, sai dai shi sashen ilimi da kuma kwalejin ilimi ba kowa ne yake son ya karanta bangaren ilimin ba, domin ya san maganar koyarwa ce.

Wani binciken da aka yi a shekarar 2015, na wadanda ke son shiga jami’oi; an samu kasa da kashi biyar daga cikin 1, 700,000 na wadanda suke son sashen ilmi, ba don komai ba sai don ba su da sha’awar yin aikin koyarwa.

Rashin tsare-tsaren aikin koyarwa masu nagarta yasa kwararrun da suka karanta sashen koyarwa, suka koma wasu wuraren da ake kula da hakkin ma’aikata daidai gwargwado, ko shakka babu irin hakan ne ke sa su ki maida hankalinsu kamar yadda ya dace ga lamarin aikin nasu na koyarwa.

Batun mafi karanci albashi a Nijeriya a lokacin da yana Naira 18,000, zai yi matukar wuya ga masu iyali su iya tafiyar da gida kamar yadda ya dace, kamar a bangaren tura ‘ya’yansu makaranta, saboda tsadar kudin makarantar da na littattafai da dai sauran makamantansu.

Littattafan da suka dace su rika taimaka wa dalibai wajen kara fahimtar abubuwan da ake koya masu, abu biyu ne a nan; na farko ko dai su kasance suna da wuyar samuwa ko kuma akwai dan karan tsada, ga su daliban ko malaman su saya su yi amfani da su.

Da Zarar an gano dalilan da suke sa ake samun matsaloli, duk abin da ake hange bai wuce a samu maganin matsalolin ba tare da bata lokaci.

Wannan dalili ne ya sa Johnson Olawale ya samar da hanyoyin da za a yi amafani da su wajen magance matsalolin da suke shafar ilimi a Nijeriya.

Matakin farko da ya dace a yi amafani da shi wajen kawo gyara kan matsalar ilimi a Nijeriya, wukar da naman na hannun gwamnati. Da akwai bukatar daukar matakai wadanda suka dace kasancewar su dole sai da su lamarin zai gyaru, idan har ana fatan a samu ceto sashen na ilimi.

Gwamantocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, akwai bukatar su kara zage damtse, don ganin sun daidaita tare da gyara matsayin ilimi ya kasance a matsayin iri daya da na sauran kasashe.

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.