ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ilimi

Makarantu da dama a halin yanzu, ba su da kayan aikin da ya kamata a ce suna da su, musamman domin taimaka wa koyarwar ta kasance cikin sauki.

Haka nan, idan ana maganar darussan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha, makarantun da suke da wadannan kayan aiki har gara ma a ce ba su da su; sakamakon rashin ingancinsu.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • Badaƙalar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kazali, dakunan karatu babu littattafan zamani da mukalu da kuma mujallun da za su taimaka wa harkokin koyo da koyarwar.

ADVERTISEMENT

Rashin tarbiyya na taimakawa wajen aikata magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, fyade da sauransu, wadanda ke taimakawa wajen gurgunta ci gaban ilimi.

Bincike ya gano cewa, akwai wasu cibiyoyin rubuta jarabawa; inda iyaye ke ba da kudi, domin ‘ya’yansu su samu sakamako mai kyau a jarrabawar kammala sakandare tare kuma da samun makin da ya dace, don samun cancantar shiga jami’a ko sauran makarantun da ke gaba da sakarandire.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

Har ila yau, rashin kulawar iyaye shi ne babban abin da ya sa ake haduwa ko samun nakasu a bangaren ilimi. Domin kuwa, su ne garkuwa wajen kulawa da rayuwar ‘ya’yansu, musamman ta fuskar ba su tarbiyya da karatunsu da kuma sauran al’amuran rayuwarsu.

Akwai abubuwan da suke taimaka wa malamai wajen aikinsu na koyarwa, wadanda da ma da su ne suke amfani wajen jan hankalin dalibai; don mayar da hankalinsu kan abubuwan da ake koya masu.

Wadannan abubuwa sun hada da wadanda za su ji da na gani, littattafai, komfuta da sauransu, ba a samar wa malamai irin wadannan kayayyakin da za su taimaka musu wajen gudanar da aikinsu daga karshe, sai koyarwar ta zamar musu da wahala.

Babu wani tsarin ilimi da aka sama wa malamai, don yadda za su samar da ilimi mai nagarta ga dalibai, shi ya sa yawancin makarantu ba sa iya tafiya da tsari ko wani abu mi tasiri wanda zai yi kama da irin tsarin Kasar Ingila.

Ba kamar sauran sassa ko bangare ba, inda dalibai suke rubibin samun gurbinsu na makaranta, sai dai shi sashen ilimi da kuma kwalejin ilimi ba kowa ne yake son ya karanta bangaren ilimin ba, domin ya san maganar koyarwa ce.

Wani binciken da aka yi a shekarar 2015, na wadanda ke son shiga jami’oi; an samu kasa da kashi biyar daga cikin 1, 700,000 na wadanda suke son sashen ilmi, ba don komai ba sai don ba su da sha’awar yin aikin koyarwa.

Rashin tsare-tsaren aikin koyarwa masu nagarta yasa kwararrun da suka karanta sashen koyarwa, suka koma wasu wuraren da ake kula da hakkin ma’aikata daidai gwargwado, ko shakka babu irin hakan ne ke sa su ki maida hankalinsu kamar yadda ya dace ga lamarin aikin nasu na koyarwa.

Batun mafi karanci albashi a Nijeriya a lokacin da yana Naira 18,000, zai yi matukar wuya ga masu iyali su iya tafiyar da gida kamar yadda ya dace, kamar a bangaren tura ‘ya’yansu makaranta, saboda tsadar kudin makarantar da na littattafai da dai sauran makamantansu.

Littattafan da suka dace su rika taimaka wa dalibai wajen kara fahimtar abubuwan da ake koya masu, abu biyu ne a nan; na farko ko dai su kasance suna da wuyar samuwa ko kuma akwai dan karan tsada, ga su daliban ko malaman su saya su yi amfani da su.

Da Zarar an gano dalilan da suke sa ake samun matsaloli, duk abin da ake hange bai wuce a samu maganin matsalolin ba tare da bata lokaci.

Wannan dalili ne ya sa Johnson Olawale ya samar da hanyoyin da za a yi amafani da su wajen magance matsalolin da suke shafar ilimi a Nijeriya.

Matakin farko da ya dace a yi amafani da shi wajen kawo gyara kan matsalar ilimi a Nijeriya, wukar da naman na hannun gwamnati. Da akwai bukatar daukar matakai wadanda suka dace kasancewar su dole sai da su lamarin zai gyaru, idan har ana fatan a samu ceto sashen na ilimi.

Gwamantocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, akwai bukatar su kara zage damtse, don ganin sun daidaita tare da gyara matsayin ilimi ya kasance a matsayin iri daya da na sauran kasashe.

Ilimi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Next Post
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.