• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Ilimi
0
Matsalolin Ilimi A Nijeriya Da Hanyoyin Gyara Su (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Makarantu da dama a halin yanzu, ba su da kayan aikin da ya kamata a ce suna da su, musamman domin taimaka wa koyarwar ta kasance cikin sauki.

Haka nan, idan ana maganar darussan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha, makarantun da suke da wadannan kayan aiki har gara ma a ce ba su da su; sakamakon rashin ingancinsu.

  • Yadda Wike Ya Kafa Tirihin Gudanar Da Ayyukan Ci Gaba A Abuja
  • BadaÆ™alar Bashin Kaduna: Abin Da Ya Sa Ba Mu Gayyaci el-Rufai Ba – Hon. Lawal

Kazali, dakunan karatu babu littattafan zamani da mukalu da kuma mujallun da za su taimaka wa harkokin koyo da koyarwar.

Rashin tarbiyya na taimakawa wajen aikata magudin jarabawa, shiga kungiyar asiri, fyade da sauransu, wadanda ke taimakawa wajen gurgunta ci gaban ilimi.

Bincike ya gano cewa, akwai wasu cibiyoyin rubuta jarabawa; inda iyaye ke ba da kudi, domin ‘ya’yansu su samu sakamako mai kyau a jarrabawar kammala sakandare tare kuma da samun makin da ya dace, don samun cancantar shiga jami’a ko sauran makarantun da ke gaba da sakarandire.

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

Har ila yau, rashin kulawar iyaye shi ne babban abin da ya sa ake haduwa ko samun nakasu a bangaren ilimi. Domin kuwa, su ne garkuwa wajen kulawa da rayuwar ‘ya’yansu, musamman ta fuskar ba su tarbiyya da karatunsu da kuma sauran al’amuran rayuwarsu.

Akwai abubuwan da suke taimaka wa malamai wajen aikinsu na koyarwa, wadanda da ma da su ne suke amfani wajen jan hankalin dalibai; don mayar da hankalinsu kan abubuwan da ake koya masu.

Wadannan abubuwa sun hada da wadanda za su ji da na gani, littattafai, komfuta da sauransu, ba a samar wa malamai irin wadannan kayayyakin da za su taimaka musu wajen gudanar da aikinsu daga karshe, sai koyarwar ta zamar musu da wahala.

Babu wani tsarin ilimi da aka sama wa malamai, don yadda za su samar da ilimi mai nagarta ga dalibai, shi ya sa yawancin makarantu ba sa iya tafiya da tsari ko wani abu mi tasiri wanda zai yi kama da irin tsarin Kasar Ingila.

Ba kamar sauran sassa ko bangare ba, inda dalibai suke rubibin samun gurbinsu na makaranta, sai dai shi sashen ilimi da kuma kwalejin ilimi ba kowa ne yake son ya karanta bangaren ilimin ba, domin ya san maganar koyarwa ce.

Wani binciken da aka yi a shekarar 2015, na wadanda ke son shiga jami’oi; an samu kasa da kashi biyar daga cikin 1, 700,000 na wadanda suke son sashen ilmi, ba don komai ba sai don ba su da sha’awar yin aikin koyarwa.

Rashin tsare-tsaren aikin koyarwa masu nagarta yasa kwararrun da suka karanta sashen koyarwa, suka koma wasu wuraren da ake kula da hakkin ma’aikata daidai gwargwado, ko shakka babu irin hakan ne ke sa su ki maida hankalinsu kamar yadda ya dace ga lamarin aikin nasu na koyarwa.

Batun mafi karanci albashi a Nijeriya a lokacin da yana Naira 18,000, zai yi matukar wuya ga masu iyali su iya tafiyar da gida kamar yadda ya dace, kamar a bangaren tura ‘ya’yansu makaranta, saboda tsadar kudin makarantar da na littattafai da dai sauran makamantansu.

Littattafan da suka dace su rika taimaka wa dalibai wajen kara fahimtar abubuwan da ake koya masu, abu biyu ne a nan; na farko ko dai su kasance suna da wuyar samuwa ko kuma akwai dan karan tsada, ga su daliban ko malaman su saya su yi amfani da su.

Da Zarar an gano dalilan da suke sa ake samun matsaloli, duk abin da ake hange bai wuce a samu maganin matsalolin ba tare da bata lokaci.

Wannan dalili ne ya sa Johnson Olawale ya samar da hanyoyin da za a yi amafani da su wajen magance matsalolin da suke shafar ilimi a Nijeriya.

Matakin farko da ya dace a yi amafani da shi wajen kawo gyara kan matsalar ilimi a Nijeriya, wukar da naman na hannun gwamnati. Da akwai bukatar daukar matakai wadanda suka dace kasancewar su dole sai da su lamarin zai gyaru, idan har ana fatan a samu ceto sashen na ilimi.

Gwamantocin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi, akwai bukatar su kara zage damtse, don ganin sun daidaita tare da gyara matsayin ilimi ya kasance a matsayin iri daya da na sauran kasashe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiMatsaloli
ShareTweetSendShare
Previous Post

Laifukan Shafin Intanet Na Ci Gaba Da Ci Wa ‘Yan Nijeriya Tuwo A Kwarya

Next Post

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Related

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)
Ilimi

Abinda Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (9)

17 hours ago
AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
Ilimi

AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

1 week ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

2 weeks ago
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima
Ilimi

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

2 weeks ago
Next Post
Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

Aikin Bututun Gas Na AKK Zai Bunƙasa Tattalin Arziƙin Arewacin Nijeriya – Minista

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.