• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Sharhi:Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da rahoton yadda ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta gudanar da wani aikin farfaganda a asirce a yayin barkewar annobar COVID-19. Bisa ga rahoton, Reuters ya gano wasu shafuka a kalla 300 da aka bude ta kafar sada zumunta na X (wato Twitter a baya), wadanda suka yi ta yada karairayi na shafa wa alluran rigakafi kirar kamfanin Sinovac na kasar Sin kashin kaji. Shafukan dai suna karkashin jagorancin sojojin kasar Amurka, kuma kusan an bude dukansu ne a shekarar 2020. An fi gudanar da aikin a kasar Philippines, baya ga wasu kasashe maso tasowa da ke tsakiyar Asiya da ma Gabas ta tsakiya ma da aikin ya shafa. 

Sakamakon wannan aikin, mutane kalilan ne suka karbi rigakafin a kasar Phlippines, wato daga cikin mutanen kasar miliyan 114, kimanin miliyan 2.1 ne kawai aka yi wa cikakkun rigakafin. Kakakin tsohon shugaban kasar ta Phlippines Harry Roque, ya bayyana ta kafar sada zumunta cewa, “Sama da ‘yan kasar dubu 60 suka halaka sakamakon annobar, wadanda ta yiwu su tsira da rayukansu idan da ba bu wannan mummunan aikin farfagandan da aka gudanar a kan rigakafi na Sinovac.”

  • Shugaba Xi Na Kasar Sin Ya Amsa Wasikar Da Mutanen Gundumar Jingning Suka Aika Masa
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Murna Ga Makon Yin Cudanya Tsakanin Matasan Sin Da Amurka 

A hakika, rigakafin Sinovac rigakafi ne daya kacal da kasar Philippines ta iya samu a wancan lokaci. Bayan barkewar annobar, kasar Sin ta rungumi ra’ayin nan na “gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya”, inda ta yi kokarin samar da gudummawar kayayyakin kandagarkin cutar ga sassan kasa da kasa, ta kuma sanar da bai wa dukkanin kasashen duniya damar yin amfani da alluran rigakafin da ta hada idan ta kammala nazarinta, don tabbatar da kasashe masu tasowa sun iya samun rigakafin da suke bukata. A watan Faburairun shekarar 2021, rukunin farko na gudummawar alluran rigakafin da kasar Sin ta samar wa kasar Philippines ya isa birnin Manila, babban birnin kasar, wanda ya kasance allurai na farko da kasar ta samu tun bayan barkewar annobar. Sai dai a yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalar karancin rigakafin, ita Amurka ta rika adana alluran da ta hada saboda manufar “fifikon kasar Amurka a kan sauran kasashen duniya” da ta aiwatar, matakin da ya bar dimbin rigakafin da dama suka lalace a banza, rigakafin da ka iya taimakawa wajen ceton dimbin rayukan al’umma.

Rahoton na Reuters ya jawo fushi daga bangarori daban daban. Mr. Harry Roque ya ce, idan Amurka ba ta son samar da rigakafinta ga Philippines, to, shi ke nan, amma me ya sa ta shafa kashin kaji ga rigakafin da sauran kasashe suka samar. A nata bangare, hukumar lafiya ta duniya WHO a martanin da ta yi, ta jaddada cewa, “rigakafin Sinovac yana da inganci, kuma yana iya magance nuna alamu masu tsanani, kai har mutuwa sakamakon cutar”. Hukumar ta kuma yi nuni da cewa, “Mai da rigakafi a matsayin makami na siyasa, zai iya haifar da mummunan sakamako.”

Abin hakan yake, yada karairayi zai iya haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma. Amma a zahiri dai, ba lafiyar al’umma ba ce ke jawo hankalin Amurka. Wani jami’in kasar Amurkan da ya sa hannu a aikin ya ce, “Ba ta fuskar mahangar lafiyar al’umma muke kallon batun ba, a’a, abin da ke jan hankalinmu shi ne ta yaya za mu jefa kasar Sin cikin halin kaka-nika-yi.” Rahoton na Reuters ya kara da cewa, dalilin da ya sa Amurka ta aiwatar da wannan aiki shi ne, sabo da tana jin tsoron tasirin matakin kasar Sin na rarraba rigakafinta ga kasashen duniya. Wani jami’in kasar da yake da hannu a aikin ya ce, “Ba mu kyauta ba wajen rarraba rigakafinmu ga kawayenmu, saboda haka abin da kawai muka iya yi shi ne mu shafa wa rigakafin kasar Sin bakin fenti.”

Labarai Masu Nasaba

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

A yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita kuma Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takarar ta ta farko, lamarin da ya sa ta dauki matakai na dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Ba kawai ta fannin rigakafin da kasar Sin ta samar ba, har ma da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma motocin lantarki da kasar ke samarwa, wadanda ke samun karbuwa daga kasa da kasa.

In mun dauki misalin Afirka, Sin da kasashen Afirka suna ta inganta hadin gwiwarsu tare da cimma gaggaruman nasarori. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke da alaka da batun “sabon salon mulkin mallaka”, da “tarkon bashi”, da “barazana daga kasar Sin” a rahotannin da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke watsawa.

Tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya taba bayyanawa a fili cewa, “Muna karya da yaudara da sata…Mun kuma samar da darasi na koyar da wannan.” Sau tari hakikanan abubuwan da suka faru sun shaida cewa, dabarar Amurka ce ta yada karairayi ta kafofin sada zumunta, a yunkurinta na shafa wa wasu kasashe kashin kaji.

Sai dai shafa bakin fenti ga sauran kasashe ba zai “sake daga martabar Amurka” ba, illa ya shaida yadda take nuna fin karfi da ma rashin amana. Kasa mai girma irin Amurka, kamata ya yi ta yi abin da ya dace. Me zai hana ta mai da hankali wajen gudanar da ayyuka masu ma’ana, da za su amfani kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, maimakon yada karairayi?

Jama’a, shawara a gare ku kuma ita ce, ku yi hankali a lokacin da ku ke karanta rahotannin da ke shafa wa kasar Sin bakin fenti. (Mai zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCOVID-19SINOVAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kar Ku Damu Ba Wata Babbar Gobara Ba ce – Matatar Dangote 

Next Post

Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Related

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!
Ra'ayi Riga

Bai Kamata a Rika Kai wa Fararen Hula Hari Ba!

3 days ago
Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
Ra'ayi Riga

Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne

3 days ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

1 week ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

1 week ago
Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”
Ra'ayi Riga

Manufar Raya Biranen Kasar Sin: Ba Wai Kawai a Tabbatar Da “Tsayi” Ba Ne Har Ma Da “Zafi”

1 week ago
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba
Ra'ayi Riga

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

2 weeks ago
Next Post
Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Karya

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.