ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi:Karya Fure Take Ba Ta ‘Ya’ya

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Karya

A kwanakin baya, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da rahoton yadda ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta gudanar da wani aikin farfaganda a asirce a yayin barkewar annobar COVID-19. Bisa ga rahoton, Reuters ya gano wasu shafuka a kalla 300 da aka bude ta kafar sada zumunta na X (wato Twitter a baya), wadanda suka yi ta yada karairayi na shafa wa alluran rigakafi kirar kamfanin Sinovac na kasar Sin kashin kaji. Shafukan dai suna karkashin jagorancin sojojin kasar Amurka, kuma kusan an bude dukansu ne a shekarar 2020. An fi gudanar da aikin a kasar Philippines, baya ga wasu kasashe maso tasowa da ke tsakiyar Asiya da ma Gabas ta tsakiya ma da aikin ya shafa. 

Sakamakon wannan aikin, mutane kalilan ne suka karbi rigakafin a kasar Phlippines, wato daga cikin mutanen kasar miliyan 114, kimanin miliyan 2.1 ne kawai aka yi wa cikakkun rigakafin. Kakakin tsohon shugaban kasar ta Phlippines Harry Roque, ya bayyana ta kafar sada zumunta cewa, “Sama da ‘yan kasar dubu 60 suka halaka sakamakon annobar, wadanda ta yiwu su tsira da rayukansu idan da ba bu wannan mummunan aikin farfagandan da aka gudanar a kan rigakafi na Sinovac.”

  • Shugaba Xi Na Kasar Sin Ya Amsa Wasikar Da Mutanen Gundumar Jingning Suka Aika Masa
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Murna Ga Makon Yin Cudanya Tsakanin Matasan Sin Da Amurka 

A hakika, rigakafin Sinovac rigakafi ne daya kacal da kasar Philippines ta iya samu a wancan lokaci. Bayan barkewar annobar, kasar Sin ta rungumi ra’ayin nan na “gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya”, inda ta yi kokarin samar da gudummawar kayayyakin kandagarkin cutar ga sassan kasa da kasa, ta kuma sanar da bai wa dukkanin kasashen duniya damar yin amfani da alluran rigakafin da ta hada idan ta kammala nazarinta, don tabbatar da kasashe masu tasowa sun iya samun rigakafin da suke bukata. A watan Faburairun shekarar 2021, rukunin farko na gudummawar alluran rigakafin da kasar Sin ta samar wa kasar Philippines ya isa birnin Manila, babban birnin kasar, wanda ya kasance allurai na farko da kasar ta samu tun bayan barkewar annobar. Sai dai a yayin da kasashe masu tasowa ke fama da matsalar karancin rigakafin, ita Amurka ta rika adana alluran da ta hada saboda manufar “fifikon kasar Amurka a kan sauran kasashen duniya” da ta aiwatar, matakin da ya bar dimbin rigakafin da dama suka lalace a banza, rigakafin da ka iya taimakawa wajen ceton dimbin rayukan al’umma.

ADVERTISEMENT

Rahoton na Reuters ya jawo fushi daga bangarori daban daban. Mr. Harry Roque ya ce, idan Amurka ba ta son samar da rigakafinta ga Philippines, to, shi ke nan, amma me ya sa ta shafa kashin kaji ga rigakafin da sauran kasashe suka samar. A nata bangare, hukumar lafiya ta duniya WHO a martanin da ta yi, ta jaddada cewa, “rigakafin Sinovac yana da inganci, kuma yana iya magance nuna alamu masu tsanani, kai har mutuwa sakamakon cutar”. Hukumar ta kuma yi nuni da cewa, “Mai da rigakafi a matsayin makami na siyasa, zai iya haifar da mummunan sakamako.”

Abin hakan yake, yada karairayi zai iya haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma. Amma a zahiri dai, ba lafiyar al’umma ba ce ke jawo hankalin Amurka. Wani jami’in kasar Amurkan da ya sa hannu a aikin ya ce, “Ba ta fuskar mahangar lafiyar al’umma muke kallon batun ba, a’a, abin da ke jan hankalinmu shi ne ta yaya za mu jefa kasar Sin cikin halin kaka-nika-yi.” Rahoton na Reuters ya kara da cewa, dalilin da ya sa Amurka ta aiwatar da wannan aiki shi ne, sabo da tana jin tsoron tasirin matakin kasar Sin na rarraba rigakafinta ga kasashen duniya. Wani jami’in kasar da yake da hannu a aikin ya ce, “Ba mu kyauta ba wajen rarraba rigakafinmu ga kawayenmu, saboda haka abin da kawai muka iya yi shi ne mu shafa wa rigakafin kasar Sin bakin fenti.”

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A yayin da kasar Sin ke dada bunkasa, ita kuma Amurka ta yi kuskure har ta dauki kasar Sin a matsayin babbar abokiyar takarar ta ta farko, lamarin da ya sa ta dauki matakai na dakile kasar Sin daga dukkan fannoni, ciki har da fannin yada labarai. Ba kawai ta fannin rigakafin da kasar Sin ta samar ba, har ma da shawarar “ziri daya da hanya daya”, da ma motocin lantarki da kasar ke samarwa, wadanda ke samun karbuwa daga kasa da kasa.

In mun dauki misalin Afirka, Sin da kasashen Afirka suna ta inganta hadin gwiwarsu tare da cimma gaggaruman nasarori. Amma Amurka wadda ta dade tana nuna fin karfi a duniya ba ta ji dadin hakan ba, don haka ma muke ta kara karanta rahotanni da ke da alaka da batun “sabon salon mulkin mallaka”, da “tarkon bashi”, da “barazana daga kasar Sin” a rahotannin da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke watsawa.

Tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya taba bayyanawa a fili cewa, “Muna karya da yaudara da sata…Mun kuma samar da darasi na koyar da wannan.” Sau tari hakikanan abubuwan da suka faru sun shaida cewa, dabarar Amurka ce ta yada karairayi ta kafofin sada zumunta, a yunkurinta na shafa wa wasu kasashe kashin kaji.

Sai dai shafa bakin fenti ga sauran kasashe ba zai “sake daga martabar Amurka” ba, illa ya shaida yadda take nuna fin karfi da ma rashin amana. Kasa mai girma irin Amurka, kamata ya yi ta yi abin da ya dace. Me zai hana ta mai da hankali wajen gudanar da ayyuka masu ma’ana, da za su amfani kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa, maimakon yada karairayi?

Jama’a, shawara a gare ku kuma ita ce, ku yi hankali a lokacin da ku ke karanta rahotannin da ke shafa wa kasar Sin bakin fenti. (Mai zane:Mustapha Bulama)

Karya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy
Karya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

Majalisa Ta shiga Taron Gaggawa Kan Batun Saya Wa Shugaba Ƙasa Sabon Jirgi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.