• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Humaira Ta Mayar Da Martani Kan Sace Mahaifiyar Rarara

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
aisha humaira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaruma a masana’antar Kannywood, kuma ta kusa da mawaki Dauda Kahutu Rarara, Aisha Humaira ta mayar da martani kan wadanda suke yi wa mahaifiyar mawakin da barayi suka sace a gidanta da ke garin Kahutu na Jihar Katsina muguwar fata, dangane wannan jarabawa da ta same ta.

Humaira a wani faifan bidiyo da ta dora a shafinta na Tik Tok ta fara da godiya da fatan alheri ga wadanda suka nuna damuwarsu kuma suka jajanta wa Rarara kan wannan iftila’in da ya samu mahaifiyarsa.
Daga nan sai ta ce tana matukar mamaki da kaico kan wasu mutane da suke yi wa mahaifiyar mawakin muguwar fata don kawai Rarara ya yi wani abin da ya bata masu rayuwa.

  • Ko Rarara Zai Iya Biyan Naira Miliyan 900 Kuɗin Fansar Mahaifiyarsa?
  • Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa

Ta tabbatar da cewar duk wanda ya san halayyar mahaifiyar mawakin ba zai yi mata wani fata mai muni ba, saboda bai war Allah ce da ta rike addinin Musulunci hannu bibiyu kuma take salatin ga Annabi a mafi yawan lokuta.

Aisha ta kara da cewar mahaifiyar mawakin a ko da yaushe tana yi masa nasiha kan ya ciyar da mutane daga cikin abin da Allah ya hore masa na dukiy,a domin kuwa duk abin da ka bai wa wani a nan duniya Allah zai biya ka a ranar gobe kiyama.

A cewarta, takan dinga yi masa nasiha tana cewa ina za ka kai kudin da Allah ya hore maka idan har ba ka taimaki al’ummar Annabi ba, kasani Allah ya ba ka wannan dukiya ne domin wasu su samu ta hanyarka ba don ka dinga ci kai kadai ba.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Dangane da zamanta a kauyen Kahutu kuwa, Aisha ta tabbatar da cewa babu yanda Rarara bai yi da mahaifiyar tasa ba kan ta koma Kano da zama, amma ta ki yarda, inda ta nuna ta fi jin dadin zama a cikin ‘yan’uwa da abokan arziki da aka taso tare tun ana yara.

Humaira ta bukaci mutane da su dinga yi wa iyayen wasu fatan alheri domin kuwa duk abin da ka yi wa iyayen wasu shi za a yi wa naka iyayen, kuma babu wanda ya isa ya gujewa kaddara, duk abin da Allah ya nufa kan mutum dole sai ya faru komai dabarar wannan mutumin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaRararaTa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

Next Post

Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma’aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

3 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

4 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma’aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma'aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.