ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Humaira Ta Mayar Da Martani Kan Sace Mahaifiyar Rarara

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
aisha humaira

Jaruma a masana’antar Kannywood, kuma ta kusa da mawaki Dauda Kahutu Rarara, Aisha Humaira ta mayar da martani kan wadanda suke yi wa mahaifiyar mawakin da barayi suka sace a gidanta da ke garin Kahutu na Jihar Katsina muguwar fata, dangane wannan jarabawa da ta same ta.

Humaira a wani faifan bidiyo da ta dora a shafinta na Tik Tok ta fara da godiya da fatan alheri ga wadanda suka nuna damuwarsu kuma suka jajanta wa Rarara kan wannan iftila’in da ya samu mahaifiyarsa.
Daga nan sai ta ce tana matukar mamaki da kaico kan wasu mutane da suke yi wa mahaifiyar mawakin muguwar fata don kawai Rarara ya yi wani abin da ya bata masu rayuwa.

  • Ko Rarara Zai Iya Biyan Naira Miliyan 900 Kuɗin Fansar Mahaifiyarsa?
  • Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa

Ta tabbatar da cewar duk wanda ya san halayyar mahaifiyar mawakin ba zai yi mata wani fata mai muni ba, saboda bai war Allah ce da ta rike addinin Musulunci hannu bibiyu kuma take salatin ga Annabi a mafi yawan lokuta.

ADVERTISEMENT

Aisha ta kara da cewar mahaifiyar mawakin a ko da yaushe tana yi masa nasiha kan ya ciyar da mutane daga cikin abin da Allah ya hore masa na dukiy,a domin kuwa duk abin da ka bai wa wani a nan duniya Allah zai biya ka a ranar gobe kiyama.

A cewarta, takan dinga yi masa nasiha tana cewa ina za ka kai kudin da Allah ya hore maka idan har ba ka taimaki al’ummar Annabi ba, kasani Allah ya ba ka wannan dukiya ne domin wasu su samu ta hanyarka ba don ka dinga ci kai kadai ba.

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Dangane da zamanta a kauyen Kahutu kuwa, Aisha ta tabbatar da cewa babu yanda Rarara bai yi da mahaifiyar tasa ba kan ta koma Kano da zama, amma ta ki yarda, inda ta nuna ta fi jin dadin zama a cikin ‘yan’uwa da abokan arziki da aka taso tare tun ana yara.

Humaira ta bukaci mutane da su dinga yi wa iyayen wasu fatan alheri domin kuwa duk abin da ka yi wa iyayen wasu shi za a yi wa naka iyayen, kuma babu wanda ya isa ya gujewa kaddara, duk abin da Allah ya nufa kan mutum dole sai ya faru komai dabarar wannan mutumin.

Aisha humaira
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
Aisha humaira
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Za’a Dakatar Da Wasa A Farkon Minti 10 Na Kowane Wasa A Kasar Argentina Saboda Girmama Messi
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Ahanor Kan Fam Miliyan 40

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Aisha humaira
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma’aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma'aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.