• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aisha Humaira Ta Mayar Da Martani Kan Sace Mahaifiyar Rarara

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
aisha humaira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jaruma a masana’antar Kannywood, kuma ta kusa da mawaki Dauda Kahutu Rarara, Aisha Humaira ta mayar da martani kan wadanda suke yi wa mahaifiyar mawakin da barayi suka sace a gidanta da ke garin Kahutu na Jihar Katsina muguwar fata, dangane wannan jarabawa da ta same ta.

Humaira a wani faifan bidiyo da ta dora a shafinta na Tik Tok ta fara da godiya da fatan alheri ga wadanda suka nuna damuwarsu kuma suka jajanta wa Rarara kan wannan iftila’in da ya samu mahaifiyarsa.
Daga nan sai ta ce tana matukar mamaki da kaico kan wasu mutane da suke yi wa mahaifiyar mawakin muguwar fata don kawai Rarara ya yi wani abin da ya bata masu rayuwa.

  • Ko Rarara Zai Iya Biyan Naira Miliyan 900 Kuɗin Fansar Mahaifiyarsa?
  • Muna Jaddada Kiran A Tsame Masarautunmu Daga Rikicin Siyasa

Ta tabbatar da cewar duk wanda ya san halayyar mahaifiyar mawakin ba zai yi mata wani fata mai muni ba, saboda bai war Allah ce da ta rike addinin Musulunci hannu bibiyu kuma take salatin ga Annabi a mafi yawan lokuta.

Aisha ta kara da cewar mahaifiyar mawakin a ko da yaushe tana yi masa nasiha kan ya ciyar da mutane daga cikin abin da Allah ya hore masa na dukiy,a domin kuwa duk abin da ka bai wa wani a nan duniya Allah zai biya ka a ranar gobe kiyama.

A cewarta, takan dinga yi masa nasiha tana cewa ina za ka kai kudin da Allah ya hore maka idan har ba ka taimaki al’ummar Annabi ba, kasani Allah ya ba ka wannan dukiya ne domin wasu su samu ta hanyarka ba don ka dinga ci kai kadai ba.

Labarai Masu Nasaba

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Dangane da zamanta a kauyen Kahutu kuwa, Aisha ta tabbatar da cewa babu yanda Rarara bai yi da mahaifiyar tasa ba kan ta koma Kano da zama, amma ta ki yarda, inda ta nuna ta fi jin dadin zama a cikin ‘yan’uwa da abokan arziki da aka taso tare tun ana yara.

Humaira ta bukaci mutane da su dinga yi wa iyayen wasu fatan alheri domin kuwa duk abin da ka yi wa iyayen wasu shi za a yi wa naka iyayen, kuma babu wanda ya isa ya gujewa kaddara, duk abin da Allah ya nufa kan mutum dole sai ya faru komai dabarar wannan mutumin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaRararaTa'addanci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Wang Lili Ke Kiyaye Neman Cimma Nasara A Wasan Kwallon Kwando

Next Post

Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma’aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

Related

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

4 days ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

4 days ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 week ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

2 weeks ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

1 month ago
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

1 month ago
Next Post
Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma’aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

Majilisar Wakilai Zata Yi Wa Ma'aikatar Mata Titsiye Kan Badaƙalar Biliyan ₦1.5b

LABARAI MASU NASABA

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

July 9, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC

July 9, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.