• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karkatar Da Goron Sallah: Ku Dawo Da Kuɗin Ma’aikata Ko Mu Hukunta Ku” – Gwamnan Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
in Labarai, Siyasa
0
Karkatar Da Goron Sallah: Ku Dawo Da Kuɗin Ma’aikata Ko Mu Hukunta Ku” – Gwamnan Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya umurci jami’an ƙananan hukumomi da hukumomin ilimi a ƙananan hukumomi da su gaggauta dawo da dubu 30 kuɗin goron Sallah da suka karkatar waɗanda gwamnati ta ba wa ma’aikata kyauta ko su fuskanci hukunci. 

Gwamnan ya yi wannan gargaɗin ne a fadar gwamnati a yayin da yake jawabi ga jama’ar da suka zo yi masa barka da kammala aikin Hajji lafiya. Ya nuna damuwa kan halayyar da wasu jami’an kuɗi suka nuna musamman a matakin ƙananan hukumomi waɗanda suka hana ma’aikatansu kuɗin goron sallar.

  • Yadda Aka Kashe Mutum Shida Da Sace Wasu Ranar Sallah A Sokoto
  • A Tsarin Mulki, Sarkin Musulmi Ba Shi Da Ikon Naɗa Wani – Gwamnatin Sokoto

Ma’aikatan ƙananan hukumomi da dama sun yi ƙorafin ba su samu kuɗin ba kamar yadda gwamna ya bayar da umurni, wasu sun ce an biya su dubu 20 bayan sallah maimakon dubu 30, wasu kuma ba su samu kuɗin ba bakidaya.

Ya ce “Na yi mamakin yadda wani zai hana ma’aikatan tallafin da muka ba su domin su samu sukunin gudanar da hidimar Sallah babba cikin tsanaki.”

“Ya zama dole waɗanda suka karkatar da kuɗin su dawo da su da gaggawa ko kuma mu ɗauki kwakkwaran matakin ladabtar da su.” Gwamnan ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Ya ƙara da cewa za su tabbatar waɗanda suka aikata laifin sun girbi abin da suka shuka domin ya zama darasi ga na baya.

Haka ma ya buƙaci shugabannin hukumomin da aka aikata irin wannan badaƙalar da su gaggauta tattara bayanan dukkanin ma’aikatan da lamarin ya shafa, su kuma tabbatar an dawo masu da haƙƙinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin HanciSakkwatoSokoto
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabuwar Shekarar Musulunci: Muna Fata Ta Zama Mai Cike Da Albarka – Gwamnan Zamfara

Next Post

Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

Related

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

2 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

4 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

6 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

7 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

15 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

19 hours ago
Next Post
Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

LABARAI MASU NASABA

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.