• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Nijeriya 6 Sun Lashe Gasar Gwanayen Koyo Ta Cambridge

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Gwanaye

Daliban Nijeriya shida, sun yi nasarar lashe gasar gwanayen koyo bayan rubuta jarrabawa a makarantar Sakandire ta Cambridge, wadda aka gudanar a watan Yunin shekarar 2023.

Darakta a ofishin hukumar kula da al’adun Birtaniya da ke Nijeriya, Lucy Pearson ce ta bayyana haka; ranar Alhamis a ofishin hukumar da ke Legas lokacin da aka bikin karramawa daliban.

  • Jami’o’i 67 Sun Yaye Dalibai 6,464 Masu Digiri Mai Daraja Ta Daya Cikin Shekara 3
  • Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje – Kungiyar Dalibai

Hukumar kula da al’adun Birtaniya tare da hadin gwiwar hukumar kula da jarrabawa ta Cambridge, su ne suka shirya wa wadannan dalibai wannan biki na karramawa; saboda irin kwazo ko hazakar da suka nuna wajen lashe gasar gwanayen koyo na makarantar ta Cambridge.

Pearson ta kara da cewa, wannan karramawa; ta kunshi daliban da suka fi samun maki mai yawa a jarabawar Turanci, a matsayin harshe na biyu.

Ta ci gaba da cewa, dalibai ‘yan Nijeriya biyu ne suka samu nasara a wannan jarrabawa ta watan Yunin shekara ta 2023, yayin da kuma wasu dalibai hudu; su ma suka taba samun irin wannan nasarar jarrabawar a watan Nuwambar 2023, dukkanin daliban shida sun fito ne daga makarantun Brookstone, James Hope College, Lagos da kuma ‘The Ambassadors Group of Schools’.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

”Oluwademilade Dabid da Omaghomi Sharon daga makarantar Brookstone, su ne suka samu wannan nasarar cin jarrabawa da aka gudanar a watan Yunin 2023, yayin kum Obodoechi Chiedozie, Fabour Chinecherem da kuma Fehintoluwa Erinayo daga makarantar James Hope College da ke Jihar Legas, sai kuma Bamidele Sharon daga makarantar Ambassadors Group of Schools, su ma suka samu irin wannan nasara a watan Nuwambar 2023.

Daraktar ta kara da cewa, dalibai 95 daga makarantu 37 wadanda ke hulda da hukumar al’adu ta Birtaniya; baki-dayansu sun cancanci yabo, sakamakon samun maki mai yawa; wanda ya zarta na kowa a tsakanin makarantun da hukumar ke hulda da su a Nijeriya.

Har ila yau, “Darussan sun hada da na halayyar Dan’adam, fasahar sadarwa ta zamani da kuma harkar kasuwanci.

“Ana karrama dalibai ne, wadanda suka fi samun maki mai yawa a duk jarrabawar darasi daya ta duniya.

“Bugu da kari, dalibai 71 ne a Nijeriya; suka samu wannan babbar karramawa, sakamakon samun makin da suka yi a kasar da ake bai wa kowa nasa darasin ya rubuta tasa jarabawar.

“Karramawar ba ta tsaya a nan kadai ba, domin kuwa ta hada da dalibai 48 da aka karrama da kuma wasu guda takwas da suka samu karramawar da ta fit a kowa a darussa daban-daban.

Haka nan ta bayyana cewa, “sun yi amfani da tsarin da ya fi dacewa wajen zaben wadanda suka cancanta a karrama su, sakamakon irin kwazon da suka nuna a dukkanin darussan da suka koya. Sannan, abin bai tsaya a nan ba; domin kuwa har a kowane matakin ilimi, kamar yadda ta bayyana.

Da take yin karin haske dangane da tagomashin da za a iya samu sakamakon dalilin karramawar saboda samun maki mai yawa,, Pearson ta ce a fadin duniya irin nau’o’in jarabawar da aka amince da su suna taimaka wa dalibai samun zuwa jami’o’i masu nagarta da kuma samun aiki mafi tsoka.

Ta ce kuma su kasance masu samun rayuwa mafificiya, inda ta kara nuna farin cikinta na nuna cewar ai abin alfhari ne ga ita hukumar domin yin hulda tare da makarantun wajen yadda lamarin ilimi yake a Daular Turawa da kuma au’o’in ilimin da ake da shi a Nijeriya.

Shi ma darekatan shiyya na Afirka kudu da sahara na ilimin kasa da kasa a jami’ar Cambride, Mista Juan Bisser, ya taya wadanda suka samu nasara masu koyo daga Nijeriya, saboda irin kwazon da suka samu a Nijeriya wajen jarabawar watannin Yuni da Nuwamba 2023.

Bisser ya ce shi tsarin lamarin ilimi da ya shafi koyo da koyarwa an tsara shi tare da lura sosai domin ya taimaka wa masu koyo su samu hanyar bunkasa basirarsu.

“Lamarin karramawar da tafi kowace daraja an lura ne da irin kokari ko kwazon da aka yi wanda ba kowa bane yake samu burin hakan a jarabawar da ake yi a duniya da ta shafi jami’ar Cambridge.

“Karramawar ta yi nuni da irin kwazo da maida hankali na masu koyon sanin ilimi ga kuma uwa uba jajircewa ta malamai da iyaye.

“Da ilimin da daliban suka samu, masu koyo na Cambridge sun shirya sosai wajen samun damar wasu hanyoyi wadanda ke gabansu da za su taimaka masu wajen cimma burinsu,”.

Da yake jawabi a madadin wadanda aka karrama, Oluwademilade Dabid cewa ya yi lamarin ya burge su da aka ga har sun cancanta.Ya yi kira da daliban Nijeriya su maida hankali kan karatunsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya
Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Gwanaye
Manyan Labarai

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Next Post
Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Gwanaye

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.