ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’o’i 67 Sun Yaye Dalibai 6,464 Masu Digiri Mai Daraja Ta Daya Cikin Shekara 3

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Digiri

Jami’o’i 67 a Nijeriya, sun yaye dalibai 6,464 masu daraja ta daya cikin shekaru uku daga fannonin ilimi daban-daban.

Haka zalika, masu ruwa da tsaki sun bukaci a rika samar da isassun kudade tare da mayar da hankali wajen koyar da ilimin sana’oi.

  • Masana Sun Yabawa Rawar Da Sin Ke Takawa Wajen Inganta Ilimi A Afrika
  • An Yi Kira Da Aiwatar Da Matakan Samar Da Ilimi Mai Inganci A Nahiyar Afirka

Duk da cewa, ana ta faman korafe-korafe a kan rashin isassun kudaden tafiyar da Jami’oi da rashin isassun kayan aiki da rashin isassun malamai da yawan tafiya yajin aiki da rashin ingantaccen bincike da rashin iya gudanar da mulki da tabarbarewar tsaro tare kuma da yadda wasu ke barin aikin koyarwa, suna komawa wasu wuraren da ake kulawa da hakkokinsu fiye da wuraren da suka bari.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, Jami’oin Nijeriya sun ci gaba da yaye dalibai, wadanda suka samu digiri mai daraja ta daya da yawan gaske daga kuma fannoni daban-daban.

Wannan al’amari, na tafiya ne kamar yadda aka saba yi a shekarun baya, ta yadda Jami’oi kalilan ne ke iya yaye dalibai da irin wannan sakamako, su ma din sai masu kyan gaske ne daliban kan samu wannan sakamako mai daraja ta daya.

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Sannan, Yawan yajin aikin da kungiyar malaman jami’oi ke yi tsawon lokaci, an danganta shi da rashin mayar da hankali a kan koyar daliban, hakan yasa kungiyar ta nuna cewa, a cikin irin wannan yanayi na karatu; ko kadan bai dace jami’oin su rika samar da daliban da za su samu irin wannan digiri mai daraja ta daya ba, kamar yadda wasu jami’oin da suka amsa sunansu suke samarwa ba.

Duk da irin halin ko matsalolin da jami’oin ke fuskanta, amma sai ga shi suna yaye irin wadannan dalibai wadanda suka fi taka rawar gani a jarabawar kammala jami’a.

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya nuna cewa, jami’oi 67 daga cikin 272; wadanda suka yi bikin yaye dalibansu ko na wadanda suka kammala karatunsu tare da wadanda suka riga su kammalawa a tsakanin watan Maris na 2023 zuwa 2024, an samu dalibai 6,464 da suka samu digiri mai daraja ta daya.

Kazalika, an samu wadannan alkaluma ne daga jawabin ranar bikin yaye dalibai na Mataimakan Shugabannin Jami’oin da kuma sauran masu ruwa da tsaki na wadannan jami’oi.

Jami’o’in Gwamnatin Tarayya, su ne kan gaba; inda suka yaye dalibai 3,736, wato kashi 57.79 cikin 100, na masu digiri mai daraja ta daya, sai kuma jami’o’i mallakar gwamnatocin jihohi da suke da dalibai 1,458, kashi 22.55 cikin 100, yayin da kuma jami’oi masu zaman kansu ke da dalibai 1,270 , kashi 19.64 cikin 1oo, na yawan wadannan dalibai cikin shekaru uku kacal.

Don haka, idan aka duba za a tarar cewa, Jami’oin Gwamnatin Tarayya 23, su ne kan gaba na wadanda suka samu wannan digiri mai daraja ta daya da dalibai 3,736, sannan, jami’oin jihohi 18 ke biye da su da dalibai 1,458, su kuma jami’oi masu zaman kansu 26, ke da dalibai 1,270.

Bugu da kari, binciken LEADERSHIP ya kara nuna Jami’ar Ilori da ke Jihar Kwara, ita ce kan gaba na wadanda suka kammala wannan digiri mai daraja ta daya da dalibai 450, Jami’ar Jihar Legas a matsayin ta biyu da 340, Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke Bauchi da dalibai 337, Jami’ar Ibadan da dalibai 314; Jami’ar Nijeriya ta Nsukka da dalibai 288; Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Akure da ke Jihar Ondo da dalibai 195; Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Minna da dalibai 187; Jami’ar Ahmadu Bello Zariya da dalibai 182; Jami’ar Bayero ta Kano da dalibai 180; Jami’ar Benin da dalibai 178, Jami’ar Obafemi Awolowo Ile-Ife da ke Jihar Osun da dalibai 158.

A banagaren jami’oi mallakar jihohi kuma ta Jihar Legas ce kan gaba da dalibai 282; mai bi mata kuma ita ce, Jami’ar Olabisi Onabanjo Ago Iwoye ta Jihar Ogun da dalibai 198; Jami’ar Jihar Kwara Malete da dalibai 183, Jami’ar Jihar Gombe kuma na da 116.

Har wa yau, jami’oi masu zaman kansu kuma, Jami’ar Cobenant da ke Ota a Jihar Ogun, na da yawan dalibai 283, Jami’ar Afe Babalola Ado Ekiti ta Jihar Ekiti na da dalibai 141; Jami’ar Fountain, Osogbo a Jihar Osun, na da dalibai 89; Jami’ar Bowen Iwo a Jihar Osun, na da dalibai 82, sai kuma Jami’ar Landmar Omu-Aran, a Jihar Kwara ked a dalibai 68.

A yawan alkaluman da LEADERSHIP ta bayyana, Jami’ar Abuja ta samar da masu digiri na daya da dalibai 152 daga cikin dalibai 8,144 da suka kammala nasu karatun.

Digiri
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Ilimi

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Next Post
Shugabar IMF: Kokarin Zurfafa Gyare-gyare A Kasar Sin Zai Haifar Da Karin Ci Gaban Tattalin Arzikinta

Shugabar IMF: Kokarin Zurfafa Gyare-gyare A Kasar Sin Zai Haifar Da Karin Ci Gaban Tattalin Arzikinta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.