• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daliban Nijeriya 6 Sun Lashe Gasar Gwanayen Koyo Ta Cambridge

by Idris Aliyu Daudawa
12 months ago
in Labarai
0
Daliban Nijeriya 6 Sun Lashe Gasar Gwanayen Koyo Ta Cambridge
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daliban Nijeriya shida, sun yi nasarar lashe gasar gwanayen koyo bayan rubuta jarrabawa a makarantar Sakandire ta Cambridge, wadda aka gudanar a watan Yunin shekarar 2023.

Darakta a ofishin hukumar kula da al’adun Birtaniya da ke Nijeriya, Lucy Pearson ce ta bayyana haka; ranar Alhamis a ofishin hukumar da ke Legas lokacin da aka bikin karramawa daliban.

  • Jami’o’i 67 Sun Yaye Dalibai 6,464 Masu Digiri Mai Daraja Ta Daya Cikin Shekara 3
  • Lokaci Ya Yi Da Nijeriya Za Rika Fitar Da Manja Kasashen Waje – Kungiyar Dalibai

Hukumar kula da al’adun Birtaniya tare da hadin gwiwar hukumar kula da jarrabawa ta Cambridge, su ne suka shirya wa wadannan dalibai wannan biki na karramawa; saboda irin kwazo ko hazakar da suka nuna wajen lashe gasar gwanayen koyo na makarantar ta Cambridge.

Pearson ta kara da cewa, wannan karramawa; ta kunshi daliban da suka fi samun maki mai yawa a jarabawar Turanci, a matsayin harshe na biyu.

Ta ci gaba da cewa, dalibai ‘yan Nijeriya biyu ne suka samu nasara a wannan jarrabawa ta watan Yunin shekara ta 2023, yayin da kuma wasu dalibai hudu; su ma suka taba samun irin wannan nasarar jarrabawar a watan Nuwambar 2023, dukkanin daliban shida sun fito ne daga makarantun Brookstone, James Hope College, Lagos da kuma ‘The Ambassadors Group of Schools’.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

”Oluwademilade Dabid da Omaghomi Sharon daga makarantar Brookstone, su ne suka samu wannan nasarar cin jarrabawa da aka gudanar a watan Yunin 2023, yayin kum Obodoechi Chiedozie, Fabour Chinecherem da kuma Fehintoluwa Erinayo daga makarantar James Hope College da ke Jihar Legas, sai kuma Bamidele Sharon daga makarantar Ambassadors Group of Schools, su ma suka samu irin wannan nasara a watan Nuwambar 2023.

Daraktar ta kara da cewa, dalibai 95 daga makarantu 37 wadanda ke hulda da hukumar al’adu ta Birtaniya; baki-dayansu sun cancanci yabo, sakamakon samun maki mai yawa; wanda ya zarta na kowa a tsakanin makarantun da hukumar ke hulda da su a Nijeriya.

Har ila yau, “Darussan sun hada da na halayyar Dan’adam, fasahar sadarwa ta zamani da kuma harkar kasuwanci.

“Ana karrama dalibai ne, wadanda suka fi samun maki mai yawa a duk jarrabawar darasi daya ta duniya.

“Bugu da kari, dalibai 71 ne a Nijeriya; suka samu wannan babbar karramawa, sakamakon samun makin da suka yi a kasar da ake bai wa kowa nasa darasin ya rubuta tasa jarabawar.

“Karramawar ba ta tsaya a nan kadai ba, domin kuwa ta hada da dalibai 48 da aka karrama da kuma wasu guda takwas da suka samu karramawar da ta fit a kowa a darussa daban-daban.

Haka nan ta bayyana cewa, “sun yi amfani da tsarin da ya fi dacewa wajen zaben wadanda suka cancanta a karrama su, sakamakon irin kwazon da suka nuna a dukkanin darussan da suka koya. Sannan, abin bai tsaya a nan ba; domin kuwa har a kowane matakin ilimi, kamar yadda ta bayyana.

Da take yin karin haske dangane da tagomashin da za a iya samu sakamakon dalilin karramawar saboda samun maki mai yawa,, Pearson ta ce a fadin duniya irin nau’o’in jarabawar da aka amince da su suna taimaka wa dalibai samun zuwa jami’o’i masu nagarta da kuma samun aiki mafi tsoka.

Ta ce kuma su kasance masu samun rayuwa mafificiya, inda ta kara nuna farin cikinta na nuna cewar ai abin alfhari ne ga ita hukumar domin yin hulda tare da makarantun wajen yadda lamarin ilimi yake a Daular Turawa da kuma au’o’in ilimin da ake da shi a Nijeriya.

Shi ma darekatan shiyya na Afirka kudu da sahara na ilimin kasa da kasa a jami’ar Cambride, Mista Juan Bisser, ya taya wadanda suka samu nasara masu koyo daga Nijeriya, saboda irin kwazon da suka samu a Nijeriya wajen jarabawar watannin Yuni da Nuwamba 2023.

Bisser ya ce shi tsarin lamarin ilimi da ya shafi koyo da koyarwa an tsara shi tare da lura sosai domin ya taimaka wa masu koyo su samu hanyar bunkasa basirarsu.

“Lamarin karramawar da tafi kowace daraja an lura ne da irin kokari ko kwazon da aka yi wanda ba kowa bane yake samu burin hakan a jarabawar da ake yi a duniya da ta shafi jami’ar Cambridge.

“Karramawar ta yi nuni da irin kwazo da maida hankali na masu koyon sanin ilimi ga kuma uwa uba jajircewa ta malamai da iyaye.

“Da ilimin da daliban suka samu, masu koyo na Cambridge sun shirya sosai wajen samun damar wasu hanyoyi wadanda ke gabansu da za su taimaka masu wajen cimma burinsu,”.

Da yake jawabi a madadin wadanda aka karrama, Oluwademilade Dabid cewa ya yi lamarin ya burge su da aka ga har sun cancanta.Ya yi kira da daliban Nijeriya su maida hankali kan karatunsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AwardsCambridgeStudents
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amfanin Hulba 21 Ga Lafiyar Dan’adam

Next Post

Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

Zanga-Zanga Ko Kun San Babban Dalilin Garƙame Abusalma A Kurkuku

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.