• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Mu Za A Yi Zanga-zangar Matsin Rayuwa – NLC

by Sadiq
11 months ago
in Labarai
0
Da Mu Za A Yi Zanga-zangar Matsin Rayuwa – NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Kasa NLC ta musanta rade-radin cewa ta janye daga zanga-zangar kasa da ake shirin gudanarwa a ranar 1 ga watan Agusta.

Cikin wata sanarwa da ta fitar a shafinta na X, NLC ta bayyana rahotannin a matsayin karya tare da cewa ba za ta iya janyewa daga zanga-zangar da ba ita ta shirya ba.

  • Gwamnati Ba Za Ta Yi Amfani Da Karfi Ba Akan Masu Zanga-zanga – Minista
  • Shugaba Tinubu Masoyin Arewa Ne – Gwamna Uba Sani

“Masu shirya zanga-zangar ta kasa ce kawai za su iya yanke shawarar janyewa ko ci gaba da zanga-zangar,” in ji NLC.

Sanarwar ta bayyana cewa “NLC tana da hanyoyi musamman hanyoyin yanke hukunci kan jagoranci wanda ayyukanta na masana’antu kamar zanga-zangar ke bi kafin a gudanar da irin wadannan ayyukan.”

NLC ta kuma nuna goyon bayanta ga zanga-zangar da ake shirin gudanarwa, tare da amincewa da matsin tattalin arzikin da ‘yan Nijeriya ke fuskanta saboda manufofin gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

“Kasancewar NLC da cewa ba ita ta shirya zanga-zangar ba, hakan ba ya nufin kungiyar ta manta da halin kuncin rayuwa da ‘yan Nijeriya ke ciki sakamakon munanan manufofin tattalin arziki na gwamnati,” in ji kungiyar ta NLC.

NLC ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya shiga tattaunawa da jagororin zanga-zangar domin biyan bukatunsu inda ta ba da shawarar a guji amfani da karfi wajen mayar da martani ga rashin jin dadin jama’a.

Tuni dai shugaban na Nijeriya ya roki ‘yan kasar da su janye shirin zanga-zangar da suke niyyar yi a farkon watan Agusta mai kamawa.

Ministan Watsa Labarai, Mohammed Idris ne ya shaida wa manema labarai hakan a fadar gwamnati a Abuja bayan kammala ganawarsa da shugaban kasar.

Ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ya nemi masu shirya zanga-zangar da su dakatar da ita su jira su ga matakin da zai ɗauka a kan korafe-korafensu.

Rokon na Shugaba Tinubu na zuwa ne a yayin da ake ta ci gaba da batun gudanar da zanga-zangar da aka yi wa take da ‘EndBadGovernance’, a fadin kasar musamman ma a shafukan sada zumunta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matsin RayuwaNijeriyaNlcTinubuZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Kaduna Ta Rushe Hukumar Da El-Rufai Ya Kirkiro

Next Post

Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha’anin Tsaro

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

22 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

1 hour ago
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

4 hours ago
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

20 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

21 hours ago
Next Post
Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha’anin Tsaro

Zanga-zangar Matsin Rayuwa: Gwamnoni Sun Gana Da Ribadu Kan Sha'anin Tsaro

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.